< Ayyukan Manzanni 13 >

1 A ikkilisiyar da take a Antiyok akwai waɗansu annabawa da malamai. Barnabas, Siman wanda ake kira Baƙi, Lusiyus mutumin Sairin, Manayen (wanda aka goya tare da Hiridus mai mulki), da kuma Shawulu.
Among [the people in] the congregation at Antioch there were (prophets/those who spoke messages from God) and those who taught [people about Jesus. They were] Barnabas; Simeon, who was also called Niger/Blackman; Lucius, from Cyrene [city]; Manaen, who had grown up with [King] Herod [Antipas]; and Saul.
2 Yayinda suna cikin sujada da azumi ga Ubangiji, Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Ku keɓe mini Barnabas da Shawulu domin aikin da na kira su.”
While they were worshipping the Lord and fasting, the Holy Spirit said [to them], “Appoint Barnabas and Saul to [serve] me and to [go and do] the work that I have chosen them [to do]!”
3 Saboda haka bayan suka yi azumi da addu’a, sai suka ɗibiya musu hannuwansu a kansu suka sallame su.
So they continued (to fast/to abstain from eating food) and pray. Then having put their hands on Barnabas and Saul and [praying that God would help them], they sent them off [to do what the Holy Spirit had commanded].
4 Sai su biyu da Ruhu Mai Tsarki ya aika suka gangara zuwa Selusiya suka shiga jirgin ruwa daga can zuwa Saifurus.
Barnabas and Saul, guided by the Holy Spirit, went down [from Antioch] to Seleucia [port]. From there they went by ship to Salamis [port on Cyprus Island].
5 Da suka isa Salamis, sai suka yi shelar maganar Allah a majami’un Yahudawa. Yohanna yana tare da su a matsayin mai taimakonsu.
While they were in Salamis, [they went] to the Jewish meeting places. There they proclaimed the message from God [about Jesus]. John [Mark went with them and] was helping them.
6 Suka zaga dukan tsibirin har sai da suka kai Bafos. A can suka sadu da wani mutumin Yahuda mai sihiri, annabin ƙarya, mai suna Bar-Yesu,
[The three of] them went across the entire island to Paphos [city]. There they met a magician whose name was Bar-Jesus. He was a Jew who falsely [claimed] (to be a prophet/to speak messages from God).
7 wanda yake ma’aikacin muƙaddas Sergiyus Bulus ne. Muƙaddas ɗin kuwa mai azanci ne ƙwarai, ya sa aka kira Barnabas da Shawulu don yana so ya ji maganar Allah.
He often accompanied the governor [of the island], Sergius Paulus, who was an intelligent man. The governor sent [someone] to ask Barnabas and Saul to come to him, because he wanted to hear God’s message. [So Barnabas and Saul came and told him about Jesus].
8 Amma Elimas mai sihirin nan (domin ma’anar sunansa ke nan) ya yi hamayya da maganarsu ya kuma yi ƙoƙari ya juyar da muƙaddas ɗin daga bangaskiya.
However, the magician, whose name was Elymas [in the Greek language], was opposing them. He repeatedly tried to persuade the governor not to believe [in Jesus].
9 Sai Shawulu, wanda kuma ake kira Bulus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya kafa wa Elimas ido ya ce,
Then Saul, who now called himself Paul, empowered by the Holy Spirit, looked intently at the magician and said,
10 “Kai ɗan Iblis ne abokin gāban dukan abin da yake daidai! Kana cike da kowane irin ruɗi da munafunci. Ba za ka daina karkata hanyoyin da suke daidai na Ubangiji ba?
“You [(sg)] are serving the devil and you oppose everything that is good! You are always lying [to people] and doing [other] evil things to them. (You must stop saying that the truth about the Lord [God is a lot of lies!]/When will you stop changing what is true about the Lord [God and saying] what is not true about him?) [RHQ]
11 Ga shi hannun Ubangiji yana gāba da kai. Za ka makance, kuma ba za ka ga rana ba har na wani lokaci.” Nan take, hazo da duhu suka sauko a kansa, ya yi ta lallubawa, yana neman wanda zai yi masa jagora.
Right now the Lord [God] [MTY] is going to punish you! You will become blind and not [even] be able to see light for [some] time.” At once he became [blind, as though he was] in a dark mist, and he groped about, searching for someone [to hold him by the] hand and lead him.
12 Sa’ad da muƙaddas ɗin ya ga abin da ya faru, sai ya ba da gaskiya, gama ya yi mamaki a kan da koyarwa game Ubangiji.
When the governor saw what had happened [to Elymas], he believed [in the Lord Jesus]. He was amazed by [what Paul and Barnabas] were teaching about the Lord [Jesus].
13 Bulus da abokan tafiyarsa suka tashi daga Bafos a jirgin ruwa zuwa Ferga a Famfiliya inda Yohanna ya bar su ya koma Urushalima.
[After that], Paul and the two men with him went by ship from Paphos to Perga [port] in Pamphylia [province. At Perga] John [Mark] left them and returned to [his home in] Jerusalem.
14 Daga Ferga kuwa suka ci gaba zuwa Antiyok na Fisidiya. A ranar Asabbaci sai suka shiga majami’a suka zauna.
Then Paul and Barnabas traveled [by land] from Perga, and arrived in Antioch [city] near Pisidia [district in Galatia province]. (On the Sabbath/On the Jewish rest day) they entered the synagogue/the Jewish meeting place and sat down.
15 Bayan an yi karatu daga cikin Doka, da kuma Annabawa, sai shugabannin majami’ar suka aika musu suka ce, “’Yan’uwa, in kuna da wani saƙon ƙarfafawa domin jama’a, sai ku yi.”
[Someone] read [aloud] from what [Moses had written. Then someone read from what the other] prophets [had written] [MTY]. Then the leaders of the Jewish meeting place gave [someone this] note [to take] to Paul and Barnabas: “Fellow Jews, if [one of] you wants to speak to the people [here] to encourage them, please speak [to us(exc) now].”
16 Yana miƙewa tsaye, sai Bulus ya yi musu alama da hannu ya ce, “Mutanen Isra’ila da kuma ku Al’ummai da kuke wa Allah sujada, ku saurare ni!
So Paul stood up and motioned with his right hand [so that the people would listen to him]. Then he said, “Fellow Israelis and you [non-Jewish people] who [also] worship God, [please] listen [to me]!
17 Allahn mutanen Isra’ila ya zaɓi kakanninmu; ya kuma sa mutanen suka yi bunkasa yayinda suke zama a ƙasar Masar, da iko mai girma ya fitar da su daga ƙasar,
God, whom we [(inc)] Israelis worship, chose our ancestors [to be his people], and he caused them to become very numerous while they were foreigners living in Egypt. [Then after many years], God helped them [MTY] powerfully and led them out of there.
18 ya kuma jure da halinsu har shekara arba’in a cikin hamada,
[Even though they repeatedly disobeyed him, he] cared for them for about 40 years [while they were] in the desert.
19 ya tumɓuke ƙasashe bakwai a Kan’ana ya kuma ba da ƙasarsu gādo ga mutanensa.
He [enabled the Israelis] to conquer seven tribal groups [who were then living] in Canaan [region], and he gave their land to us Israelis for us to possess.
20 Dukan wannan ya ɗauki kusan shekaru 450. “Bayan wannan, Allah ya ba su alƙalai har zuwa zamanin annabi Sama’ila.
[Our ancestors began to possess Canaan] about 450 years after [their ancestors had arrived in Egypt].” Acts 13:20b-22 “After that, God appointed leaders [to rule the Israeli people. Those leaders continued to rule our people] until the time when the prophet Samuel [ruled them].
21 Sa’an nan mutanen suka nemi a ba su sarki, Allah kuwa ya ba su Shawulu ɗan Kish, na kabilar Benyamin, wanda ya yi mulki shekaru arba’in.
Then, [while Samuel was still their leader], the people demanded that he [appoint] a king [to rule them. So] God appointed Saul, the son of Kish, from the tribe of Benjamin, [to be their king]. He [ruled them] for 40 years.
22 Bayan an kau da Shawulu, sai ya naɗa Dawuda ya zama sarkinsu. Ya kuma yi shaida game da shi cewa, ‘Na sami Dawuda ɗan Yesse, mutum ne da nake so a zuciyata; shi zai aikata dukan abin da nake so.’
After God had rejected Saul [from being king], he appointed David to be their king. God said about him, ‘I have observed that David, son of Jesse, is exactly the kind of man that I desire [IDM]. He will do [everything that] I want [him to do].’”
23 “Daga zuriyar mutumin nan ne Allah ya kawo wa Isra’ila Mai Ceto Yesu, kamar yadda ya yi alkawari.
“From [among] David’s descendants, God brought one of them, Jesus, to [us] Israeli people to save us, just like he had told [David and our other ancestors] that he would do.
24 Kafin zuwan Yesu, Yohanna ya yi wa’azin tuba da baftisma ga dukan mutanen Isra’ila.
Before Jesus began his work, John [the Baptizer] preached to all of our Israeli people [who came to him. He told them] that they should turn away from their sinful behavior [and ask God to forgive them. Then he] would baptize them.
25 Yayinda Yohanna yake kammala aikinsa ya ce, ‘Wa kuke tsammani ni nake? Ba ni ne shi ba. A’a, amma yana zuwa bayana, wanda ko takalmansa ma ban isa in kunce ba.’
When John was about to finish the work [that God gave him to do], he frequently said [to the people], ‘Do you think [RHQ] that I am [the Messiah whom God promised to send]? No, I am not. But listen! The Messiah will [soon] come. [He is so much greater than I am that] I am not [even] important enough to be his slave [MET].’”
26 “Ya ku’yan’uwa,’ya’yan Ibrahim, da ku kuma Al’ummai masu tsoron Allah, a gare mu ne fa aka aiko wannan saƙon ceto.
“Fellow Israelis, you who are descendants of Abraham, and [you non-Jewish people who] also worship God, [please listen! It is] to [all of] us that [God] has sent the message about [how he] saves people.
27 Mutanen Urushalima da masu mulkinsu ba su gane da Yesu ba, duk da haka cikin hukunta shi suka cika kalmomin annabawan da ake karantawa kowane Asabbaci.
The people who were living in Jerusalem and their rulers did not realize that this man [Jesus was the one whom God had sent to save them]. Although messages from [MTY] the prophets have been read [aloud] {someone has read [aloud] messages from [MTY] the prophets} every (Sabbath/Jewish day of rest), they did not understand [what the prophets wrote about the Messiah. So] the [Jewish leaders] condemned Jesus [to die], which was just like the prophets predicted.
28 Ko da yake ba su same shi da wani dalilin da ya kai ga hukuncin kisa ba, suka roƙi Bilatus yă sa a kashe shi.
[Many people accused Jesus of doing wicked things], but they could not prove that he had done anything for which he deserved to die. They insistently asked Pilate [the governor] to command that Jesus be executed {to command soldiers to execute Jesus}. [So Pilate did what they asked him to do].
29 Sa’ad da suka aikata duk abin da aka rubuta game da shi, sai suka saukar da shi daga itacen suka kuma sa shi a kabari.
They did [to Jesus] all the things that [the prophets long ago had] written [that people would do to] him. [They killed Jesus by nailing him to a cross. Then] his body was taken {[some people took] his body} down from the cross and placed it in a tomb.
30 Amma Allah ya tashe shi daga matattu,
However, God (raised him from the dead/caused him to live again after he had died)
31 kuma kwanaki da yawa waɗanda suka yi tafiya tare da shi daga Galili zuwa Urushalima suka gan shi. Su ne yanzu shaidu ga mutanenmu.
and for many days he [repeatedly] appeared to [his followers] who had come along with him from Galilee [province] to Jerusalem. Those [who saw him] are telling the [Jewish] people about him now.”
32 “Muna gaya muku labari mai daɗi cewa abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari,
“[Right] now we [two] are proclaiming to you this good message. We want to tell you that God has fulfilled what he promised to [our Jewish] ancestors!
33 ya cika mana, mu zuriyarsu, ta wurin tā da Yesu daga matattu. Kamar yadda yake a rubuce a cikin Zabura ta biyu cewa, “‘Kai Ɗana ne, yau na zama Uba a gare ka.’
He has now done that for us [(inc) who are] their descendants, [and also for you who are not Jews], by causing Jesus to live again. That is just like what [David] wrote in the second Psalm that [God said when he was sending his Son], You [(sg)] are my Son; Today I have shown everyone [that I really am] your Father.
34 Gaskiyar cewa Allah ya tā da shi daga matattu, a kan ba zai taɓa ruɓewa ba, an faɗe shi a cikin waɗannan kalmomi. “‘Zan ba ku tsarki da kuma tabbatattun albarkun da na yi wa Dawuda alkawari.’
[God] has (raised [the Messiah] from the dead/caused [the Messiah] to live again after he had died) and will never let him die again. [Concerning that, God] said [to our Jewish ancestors], ‘I will surely help you, as I [promised] David [that I would do].’
35 Haka kuma aka faɗa a wani wuri. “‘Ba za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba.’
So [in writing] another [Psalm, David] said this [to God about the Messiah]: ‘Because I am devoted to you and always obey [you, when I die] you [(sg)] will not let my body decay.’
36 “Gama sa’ad da Dawuda ya gama hidimar nufin Allah a zamaninsa, sai ya yi barci; aka binne shi tare da kakanninsa jikinsa kuwa ya ruɓe.
While David was living, he did what God wanted him to do. And when he died [EUP], his [body] was buried, [as] his ancestors’ [bodies had been buried], and his body decayed. [So he could not have been speaking about himself in this Psalm].
37 Amma wanda Allah ya tā da daga matattu bai ruɓa ba.
[Instead, he was speaking about Jesus. Jesus also died], but God (raised him from the dead/caused him to live again), and [therefore] his body did not decay.”
38 “Saboda haka,’yan’uwana, ina so ku san cewa ta wurin Yesu ana sanar muku da gafarar zunubi.
“Therefore, [my] fellow Israelis [and other friends], it is important for you to know that [we(exc)] are declaring to you [that God] can forgive you for your sins as a result of [what] Jesus [has done]. Because of [what] Jesus [has done], [God] considers that everyone who believes [in Jesus] is no longer guilty (OR, the record has been erased {[God] has erased the record}) concerning everything that they [have done that displeased God. But] when [God] does [that for you], it is not as a result of [your obeying] the laws [that] Moses [wrote].
39 Ta wurinsa kowa da ya gaskata an kuɓutar da shi daga dukan abin da Dokar Musa ba tă iya kuɓutar ba.
40 Ku lura kada abubuwan da annabawa suka faɗa su faru muku.
Therefore be careful that [God] does not judge you [MTY], as one of the prophets said [MTY] that God would do!
41 “‘Ku duba, ku masu ba’a, ku yi mamaki, ku hallaka, gama zan yi wani abu a zamaninku da ba za ku taɓa gaskatawa ba ko da wani ya gaya muku.’”
[The prophet wrote that God said], You who ridicule [me], you will [certainly] be astonished [when you see what I am doing], and [then] you will be destroyed. You will be astonished because I will do something [terrible to you] while you are living. You would not believe [that I would do that] even though someone told you!”
42 Bulus da Barnabas suna fita daga majami’ar ke nan, sai mutane suka gayyace su su ƙara yin maganan nan a kan waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci mai zuwa.
After Paul [finished speaking], while he and Barnabas were leaving the Jewish meeting place, [many of] the people there repeatedly requested that on the next (Sabbath/Jewish day of rest) [the two of them] should speak to them [again] about those things [that Paul had just told them].
43 Da aka sallami jama’a, Yahudawa da yawa da kuma waɗanda suka tuba suka shiga Yahudanci masu ibada suka bi Bulus da Barnabas, waɗanda suka yi magana musu suka kuma ƙarfafa su su ci gaba a cikin alherin Allah.
After they began to leave [that meeting], many [of them] went along with Paul and Barnabas. They consisted of Jews and also of non-Jews who had accepted the things that the Jews believe. Paul and Barnabas continued talking to them, and were urging them to continue [believing the message that] God kindly [forgives people’s sins because of what Jesus did].
44 A ranar Asabbaci na biye kusan dukan birnin suka taru don su ji maganar Ubangiji.
On the next Jewish rest day, most of the [people in Antioch came to] the Jewish meeting place to hear [Paul and Barnabas] speak about the Lord [Jesus].
45 Sa’ad da Yahudawa suka ga taron mutanen, sai suka cika da kishi suka yi ta munanan maganganu a kan abin da Bulus yake faɗi.
But [the leaders of] [SYN] the Jews became extremely jealous, because they saw that large crowds of [non-Jewish people were coming to hear Paul and Barnabas. So] they began to contradict the things that Paul was saying [and also] to insult [him].
46 Sai Bulus da Barnabas suka amsa musu gabagadi, suka ce, “Ya zama mana dole mu yi muku maganar Allah da farko. Da yake kun ƙi ta ba ku kuma ga kun cancanci rai madawwami ba, to, za mu juya ga Al’ummai. (aiōnios g166)
Then, speaking very boldly, Paul and Barnabas said [to those Jewish leaders], “[We two] had to speak the message from God [about Jesus] to you [Jews] first [before we proclaim it to non-Jews, because God commanded us to do that. But] you are rejecting God’s message. [By doing that], you have shown that you are not worthy (to have eternal life/to live eternally [with God]). [Therefore], we are leaving [you, and now we] will go to the non-Jewish people [to tell them the message from God]. (aiōnios g166)
47 Gama abin da Allah ya umarce mu ke nan cewa, “‘Na sa ka zama haske ga Al’ummai, don ka kawo cetona zuwa iyakokin duniya.’”
[We are doing that also] because the Lord [God] has commanded us [to do it]. He said to us, ‘I have appointed you [to reveal things about me] to non-Jewish people [MET] that will be [like] a light to them. [I have appointed] you to tell people everywhere [MTY] in the world [about the one who came] to save [them].’”
48 Sa’ad da Al’ummai suka ji haka, sai suka yi farin ciki suka ɗaukaka maganar Ubangiji; kuma duk waɗanda aka zaɓa don samun rai madawwami, suka gaskata. (aiōnios g166)
While the non-Jewish people were listening [to those words], they began to rejoice, and they repeatedly said that the message about the Lord [Jesus] was wonderful. And all of the non-Jewish people whom [God] had chosen (to have eternal [life/to live eternally with God]) believed [the message about the Lord Jesus]. (aiōnios g166)
49 Maganar Ubangiji kuwa ta bazu a dukan yankin.
[At that time, many of the believers] traveled around throughout that region. As they did that, they were proclaiming the message about the Lord [Jesus] [MTY].
50 Amma Yahudawa suka zuga waɗansu mata masu tsoron Allah masu martaba da kuma waɗansu maza masu matsayi a gari. Suka tā da tsanani ga Bulus da Barnabas, suka kore su daga yankinsu.
However, [some leaders of] [SYN] the Jews incited the most important men in the city, and [some] important/influential women who had accepted what the Jews believe, to oppose [Paul and Barnabas. So those non-Jewish people] incited [other people also] to persecute Paul and Barnabas. As a result they expelled the two men from their region.
51 Saboda haka suka karkaɗe ƙurar ƙafafunsu don shaidar a kansu suka kuwa tafi Ikoniyum.
So, [as the two apostles were leaving, they] shook the dust from their feet [to show those Jewish leaders that God had rejected them and would punish them. They left Antioch] and went to Iconium [city].
52 Masu bi kuwa suka cika da farin ciki da kuma Ruhu Mai Tsarki.
Meanwhile, the believers [in Antioch] continued to rejoice greatly, and they continued to be completely controlled by the Holy Spirit.

< Ayyukan Manzanni 13 >