< Ayyukan Manzanni 12 >
1 Kusan a wannan lokaci ne Sarki Hiridus ya kama waɗansu da suke na ikkilisiya, da niyya ya tsananta musu.
Now, at about that time, Herod the king put forth his hands to ill- treat certain members of the church;
2 Ya sa aka kashe Yaƙub, ɗan’uwan Yohanna, da takobi.
and beheaded James, the brother of John, with the sword.
3 Sa’ad da ya ga wannan ya faranta wa Yahudawa rai, sai ya kama Bitrus shi ma. Wannan ya faru kwanakin Bikin Burodi Marar Yisti.
And when he saw that it pleased the Jews, he proceeded to seize Peter also. (This was during the days of unleavened bread.)
4 Bayan ya kama shi, sai ya sa shi a kurkuku, ya danƙa shi a hannun soja hurhuɗu kashi huɗu, don su yi gadinsa. Hiridus ya yi niyyar ya yi masa shari’a a gaban mutane bayan Bikin Ƙetarewa.
He had him arrested and thrown in prison, and put under guard of sixteen soldiers. He intended, after the Passover, to bring him forth to the people.
5 Saboda haka aka tsare Bitrus a kurkuku, amma ikkilisiya ta nace da addu’a ga Allah dominsa.
So Peter was kept in prison, but earnest prayer to God was made by the church for him.
6 A daren da in gari ya waye da Hiridus yake niyyar kawo shi domin a yi masa shari’a, Bitrus yana barci tsakanin sojoji biyu, daure da sarƙoƙi biyu, masu gadi kuma suna bakin ƙofa.
Now when Herod was about to bring him forth, on that very night, while Peter was sleeping between two soldiers, bound with chains, and sentries before the door were guarding the prison,
7 Ba zato ba tsammani sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana haske kuma ya haskaka a ɗakin. Ya bugi Bitrus a gefe ya kuma tashe shi ya ce, “Maza, ka tashi!” Sarƙoƙin kuwa suka zube daga hannuwansa.
suddenly an angel of the Lord stood by him, and a light shone in the cell. Striking Peter on the side, he woke him saying, "Rise up quickly." At once the chains dropped from his hands.
8 Sa’an nan mala’ikan ya ce masa, “Ka sa rigunarka da takalmanka.” Bitrus kuwa ya sa. Mala’ikan ya faɗa masa cewa, “Ka yafa mayafinka ka bi ni.”
"Gird yourself," said the angel, "and put on your sandals." He did so. Then he said unto him, "Throw your cloak about you, and follow me."
9 Bitrus ya bi shi suka fita kurkukun, amma bai ma san cewa abin da mala’ikan yake yi tabbatacce ne ba; yana tsammani wahayi yake gani.
So Peter went out, following him, but did not realize that what the angel was doing was real, but supposed that he was seeing a vision.
10 Suka wuce masu gadi na fari da na biyu, suka kuma isa ƙofar ƙarfe ta shiga birni. Ƙofar kuwa ta buɗe musu da kanta, suka kuma wuce. Sa’ad da suka yi tafiya tsawon wani titi, nan take mala’ikan ya bar shi.
And when they had passed the first guard and the second, they came to the iron gate that led to the city. This opened to them of its own accord; and they went out passed on through one street; and suddenly the angel left him.
11 Sai Bitrus ya dawo hankalinsa ya ce, “Yanzu na sani ba shakka Ubangiji ne ya aiki mala’ikansa yă cece ni daga hannun Hiridus da kuma dukan mugun fatan Yahudawa.”
Peter, coming to himself, said, "Now I know for a certainty that the Lord has sent his angel and released me from the hand of Herod, and from all that the Jewish people were anticipating."
12 Da ya gane haka, sai ya tafi gidan Maryamu uwar Yohanna, wanda ake kuma kira Markus, inda mutane da yawa suka taru suna addu’a.
So, after he had thought things over, he went to the house of Mary, the mother of John, surnamed Mark, where a large number of people were assembled, praying.
13 Bitrus ya ƙwanƙwasa ƙofar waje, sai wata mai aiki a gidan da ake kira Roda ta zo tă ji ko wane ne.
When he knocked at the door of the gate, a maid servant named Rhoda came to answer.
14 Da ta gane muryar Bitrus, ta cika da murna ta gudu ta koma ba tare da ta buɗe ƙofar ba, sai ta koma a guje ta ce da ƙarfi, “Ga Bitrus a bakin ƙofa!”
And when she recognized Peter’s voice, for very joy she did not open the door, but ran in and told them that Peter was standing in front of the gate.
15 Sai suka ce mata, “Kina hauka.” Da ta nace cewa shi ne, sai suka ce, “To, lalle, mala’ikansa ne.”
"You are mad," they said. But she confidently insisted that it was so. "It is his angel," they said.
16 Amma Bitrus ya yi ta ƙwanƙwasawa. Da suka buɗe ƙofar suka kuma gan shi, sai suka yi mamaki.
Meanwhile Peter continued to knock, until at last they opened the door, and were amazed to see that it was really he.
17 Bitrus ya yi musu alama da hannunsa su yi shiru sai ya bayyana yadda Ubangiji ya fitar da shi daga kurkuku. Ya ce, “Ku gaya wa Yaƙub da kuma’yan’uwa game da wannan,” sa’an nan ya tashi ya tafi wani wuri.
He motioned to them to keep quiet, and told them how the Lord had brought him out of prison. "Tell all this to James," he said, "and to the brothers," and away he went to another place.
18 Da safe, hargitsin da ya tashi tsakanin sojojin ba ƙarami ba ne, a kan abin da ya sami Bitrus.
When morning came there was no small stir among the soldiers as to what could possibly have become of Peter.
19 Bayan Hiridus ya neme shi bai same shi ba, sai ya tuhumi masu gadin, ya kuma ba da umarni a kashe su. Sa’an nan Hiridus ya tashi daga Yahudiya ya tafi Kaisariya ya kuma yi’yan kwanaki a can.
Then Herod had search made for him, and could not find him. After sharply questioning the guards, he ordered them off to execution. He then went down from Judea to Caesarea, where he stayed for some time.
20 Yana da rashin jituwa da mutanen Taya da na Sidon; sai suka haɗa kai suka nemi ganawa da shi. Bayan suka sami goyon bayan Bilastus, amintaccen bawan sarki, sai suka nemi salama, domin sun dogara ga ƙasar sarkin don samun abincinsu.
Now Herod was violently displeased with the people of Tyre and Sidon. So they came to him, with one accord, and after conciliating Blastus, the royal chamberlain, they begged for peace because their country depended upon the king’s country for its food supply.
21 A ranar da aka shirya Hiridus, sanye da kayan sarautarsa, ya zauna a gadon sarautarsa ya kuma ya wa mutanen jawabi.
So on the appointed day, Herod put on his royal robes, and after taking his seat upon the throne, began to harangue them.
22 Suka tā da murya suka ce, “Wannan muryar wani allah ne, ba ta mutum ba.”
"The voice of a god, and not of a man," the people kept shouting.
23 Nan take, domin Hiridus bai yi wa Allah yabo ba, wani mala’ikan Ubangiji ya buge shi, tsutsotsi kuwa suka cinye shi ya kuma mutu.
Instantly an angel of the Lord smote him, because he had not given God the glory, and being eaten up by worms, he died.
24 Amma maganar Allah ta ci gaba da ƙaruwa ta kuma bazu.
But the word of God grew and multiplied;
25 Sa’ad da Barnabas da Shawulu suka kammala aikinsu, sai suka komo daga Urushalima, tare da Yohanna, wanda ake kira Markus.
and after discharging their mission, Barnabas and Saul returned from Jerusalem, bringing with them John, surnamed Mark.