< Ayyukan Manzanni 12 >
1 Kusan a wannan lokaci ne Sarki Hiridus ya kama waɗansu da suke na ikkilisiya, da niyya ya tsananta musu.
Now, about that time, Herod, the king, laid hands on some of the congregation, to afflict them.
2 Ya sa aka kashe Yaƙub, ɗan’uwan Yohanna, da takobi.
And he slew James, the brother of John, with the sword.
3 Sa’ad da ya ga wannan ya faranta wa Yahudawa rai, sai ya kama Bitrus shi ma. Wannan ya faru kwanakin Bikin Burodi Marar Yisti.
And as he saw that this was acceptable to the Jews, he went on to seize Peter also: and it was in the days of unleavened bread;
4 Bayan ya kama shi, sai ya sa shi a kurkuku, ya danƙa shi a hannun soja hurhuɗu kashi huɗu, don su yi gadinsa. Hiridus ya yi niyyar ya yi masa shari’a a gaban mutane bayan Bikin Ƙetarewa.
and having seized him, he put him in prison, delivering him to the custody of four quaternions of soldiers, intending, after the passover, to bring him out to the people.
5 Saboda haka aka tsare Bitrus a kurkuku, amma ikkilisiya ta nace da addu’a ga Allah dominsa.
In the meantime, therefore, Peter was kept in the prison; but earnest and continued prayer was made to God on his account, by the congregation.
6 A daren da in gari ya waye da Hiridus yake niyyar kawo shi domin a yi masa shari’a, Bitrus yana barci tsakanin sojoji biyu, daure da sarƙoƙi biyu, masu gadi kuma suna bakin ƙofa.
And when Herod was ready to have brought him out, even that very night, Peter was sleeping between two soldiers, bound with two chains; and the guards before the door were keeping the prison.
7 Ba zato ba tsammani sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana haske kuma ya haskaka a ɗakin. Ya bugi Bitrus a gefe ya kuma tashe shi ya ce, “Maza, ka tashi!” Sarƙoƙin kuwa suka zube daga hannuwansa.
And, behold, a messenger of the Lord presented himself, and a light shone in the house; giving Peter a blow on the side, he awoke him, saying, Arise quickly: and his chains fell off from his hands.
8 Sa’an nan mala’ikan ya ce masa, “Ka sa rigunarka da takalmanka.” Bitrus kuwa ya sa. Mala’ikan ya faɗa masa cewa, “Ka yafa mayafinka ka bi ni.”
And the messenger said to him, Gird yourself, and bind on your sandals; and he did so. And he said to him, Throw your mantle round you, and follow me.
9 Bitrus ya bi shi suka fita kurkukun, amma bai ma san cewa abin da mala’ikan yake yi tabbatacce ne ba; yana tsammani wahayi yake gani.
And going out he followed him; and he did not know that what was done by the messenger was real; but supposed that he had seen a vision.
10 Suka wuce masu gadi na fari da na biyu, suka kuma isa ƙofar ƙarfe ta shiga birni. Ƙofar kuwa ta buɗe musu da kanta, suka kuma wuce. Sa’ad da suka yi tafiya tsawon wani titi, nan take mala’ikan ya bar shi.
And passing through the first and second watch, they came to the iron gate that leads into the city; which opened to them of its own accord. And going out, they went through one street, and immediately the messenger departed from him.
11 Sai Bitrus ya dawo hankalinsa ya ce, “Yanzu na sani ba shakka Ubangiji ne ya aiki mala’ikansa yă cece ni daga hannun Hiridus da kuma dukan mugun fatan Yahudawa.”
And Peter, being come to himself, said, Now I know truly, that the Lord has sent his messenger, and has delivered me from the hand of Herod, and from all the expectations of the Jewish people.
12 Da ya gane haka, sai ya tafi gidan Maryamu uwar Yohanna, wanda ake kuma kira Markus, inda mutane da yawa suka taru suna addu’a.
And recollecting, he came to the house of Mary, the mother of John, who was surnamed Mark; where many were gathered together, praying.
13 Bitrus ya ƙwanƙwasa ƙofar waje, sai wata mai aiki a gidan da ake kira Roda ta zo tă ji ko wane ne.
And as Peter knocked at the door of the outer gate, a maiden, whose name was Rose, went to inquire who was there.
14 Da ta gane muryar Bitrus, ta cika da murna ta gudu ta koma ba tare da ta buɗe ƙofar ba, sai ta koma a guje ta ce da ƙarfi, “Ga Bitrus a bakin ƙofa!”
And knowing Peter's voice, transported with joy, she did not open the gate: but running in, told them that Peter was standing at the gate.
15 Sai suka ce mata, “Kina hauka.” Da ta nace cewa shi ne, sai suka ce, “To, lalle, mala’ikansa ne.”
And they said to her, You are distracted: but she confidently affirmed that it was so.
16 Amma Bitrus ya yi ta ƙwanƙwasawa. Da suka buɗe ƙofar suka kuma gan shi, sai suka yi mamaki.
But Peter continued knocking; and when she opened the door, they saw him, and were astonished.
17 Bitrus ya yi musu alama da hannunsa su yi shiru sai ya bayyana yadda Ubangiji ya fitar da shi daga kurkuku. Ya ce, “Ku gaya wa Yaƙub da kuma’yan’uwa game da wannan,” sa’an nan ya tashi ya tafi wani wuri.
And he made a sign to them with his hand to be silent; and related to them how the Lord had conducted him out of prison. And he aid, Inform James and the brethren of these things: and departing, he went to another place.
18 Da safe, hargitsin da ya tashi tsakanin sojojin ba ƙarami ba ne, a kan abin da ya sami Bitrus.
And as soon as it was day, there was no small tumult among the soldiers, what was become of Peter.
19 Bayan Hiridus ya neme shi bai same shi ba, sai ya tuhumi masu gadin, ya kuma ba da umarni a kashe su. Sa’an nan Hiridus ya tashi daga Yahudiya ya tafi Kaisariya ya kuma yi’yan kwanaki a can.
And Herod searching for him, and not finding him, examined the keeper, and ordered them to be led away to execution. and passing from Judea to Cesarea, he abode there.
20 Yana da rashin jituwa da mutanen Taya da na Sidon; sai suka haɗa kai suka nemi ganawa da shi. Bayan suka sami goyon bayan Bilastus, amintaccen bawan sarki, sai suka nemi salama, domin sun dogara ga ƙasar sarkin don samun abincinsu.
And he was highly incensed against the Tyrians and Sidonians; but they unanimously came before him; and gaining Blastus, the king's chamberlain, to their interest, they begged for peace; because their country was nourished by that of the king.
21 A ranar da aka shirya Hiridus, sanye da kayan sarautarsa, ya zauna a gadon sarautarsa ya kuma ya wa mutanen jawabi.
And upon a set day, Herod, being arrayed in a royal habit, and seated upon the throne, made an oration to them.
22 Suka tā da murya suka ce, “Wannan muryar wani allah ne, ba ta mutum ba.”
And the people cried out, It is the voice of a God, and not of a man!
23 Nan take, domin Hiridus bai yi wa Allah yabo ba, wani mala’ikan Ubangiji ya buge shi, tsutsotsi kuwa suka cinye shi ya kuma mutu.
But immediately a messenger of the Lord smote him, because he did not give glory to God: and being eaten with worms, he expired.
24 Amma maganar Allah ta ci gaba da ƙaruwa ta kuma bazu.
And the word of God grew and was multiplied.
25 Sa’ad da Barnabas da Shawulu suka kammala aikinsu, sai suka komo daga Urushalima, tare da Yohanna, wanda ake kira Markus.
And Barnabas and Saul, having fulfilled their ministry, returned from Jerusalem; bringing along with them John, whose surname was Mark.