< Ayyukan Manzanni 11 >
1 Manzanni da’yan’uwa ko’ina a Yahudiya suka ji cewa Al’ummai ma sun karɓi maganar Allah.
Slišali pa so aposteljni in bratje, kteri so bili v Judeji, da so tudi pogani sprejeli besedo Božjo.
2 Saboda haka sa’ad da Bitrus ya haura zuwa Urushalima, masu bin da suke da kaciya suka zarge shi
In ko je prišel Peter v Jeruzalem, prepirali so se z njim, kteri so bili iz obreze,
3 suka ce, “Ka je gidan mutanen da suke marasa kaciya ka kuwa ci tare da su.”
Govoreč: K možém neobrezanim si šel, in jedel si ž njimi.
4 Bitrus ya fara yin musu bayani dalla-dalla yadda ya faru cewa,
Peter pa začne, in izkladal jim je po vrsti, govoreč:
5 “Ina a birnin Yoffa ina addu’a, sai ga wahayi ya zo mini. Na ga ana sauko da wani abu kamar babban mayafi daga sama ta kusurwansa huɗu, ya kuma sauko inda nake.
Jaz sem v mestu Jopi molil, in videl sem v zamaknenji prikazen, da je shajala nekaka posoda, kakor velik prt, in se je za čvetere ogle spuščala z neba, in prišla noter do mene.
6 Na duba cikinsa na ga dabbobi masu ƙafa huɗu na duniya, da namun jeji, da masu ja da ciki, da kuma tsuntsayen sararin sama.
In pogledavši va-njo, opazim in ugledam štirinogate in divje in lazeče živali zemlje, in tice nebeške.
7 Sa’an nan na ji wata murya tana ce mini, ‘Bitrus, ka tashi. Ka yanka ka ci.’
In zaslišim glas, da mi pravi: Vstani, Peter, zakolji in jej!
8 “Na amsa na ce, ‘Sam, Ubangiji! Ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko marar tsabta ba.’
In rekel sem; Nikakor ne, Gospod! kajti nagnjusnega ali nečistega ni nikoli nič prišlo v usta moja.
9 “Sai muryar daga sama ta yi magana sau na biyu, ta ce, ‘Kada ka ce da abin da Allah ya tsarkake marar tsarki.’
Odgovorí pa mi glas v drugo z neba: Kar je Bog očistil, ne imej ti za nagnjusno.
10 Wannan ya faru har sau uku, sa’an nan duk aka sāke ɗauke shi zuwa sama.
To pa se je zgodilo trikrat, in zopet se je potegnilo vse na nebo.
11 “Nan take sai ga mutum uku da aka aika wurina daga Kaisariya a tsaye a ƙofar gidan da nake.
In glej, precej se trije možjé postavijo pred hišo, v kterej sem bil, poslani iz Cezareje k meni.
12 Ruhu ya ce mini kada in yi wata-wata game da tafiya tare da su. Waɗannan’yan’uwa guda shida su ma suka rako ni, muka kuwa shiga gidan mutumin.
In reče mi Duh, naj grem brez pomišljevanja ž njimi. Prišlo je pa z menoj tudi tehle šest bratov, in vstopili smo v hišo moževo.
13 Ya kuma gaya mana yadda wani mala’ika ya bayyana a gidansa ya ce masa, ‘Ka aika zuwa Yoffa a kira Siman wanda ake ce da shi Bitrus.
In povedal nam je, kako je videl angelja v hiši svojej, da je pristopil in mu rekel: Pošlji v Jopo móž, in pokliči Simona s priimkom Petra,
14 Zai kawo maka saƙo wanda ta wurinsa kai da dukan iyalinka za ku sami ceto.’
Kteri ti bo govoril besede, po kterih se boš zveličal ti in vsa hiša tvoja.
15 “Na fara magana ke nan, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu yadda ya sauko mana a farko.
Ko sem pa jel govoriti, pade sveti Duh na-nje, kakor tudi na nas v začetku.
16 Sa’an nan na tuna da abin da Ubangiji ya ce, ‘Yohanna ya yi baftisma da ruwa, amma za a yi muku baftisma daRuhu Mai Tsarki.’
Tedaj sem se spomenil besede Gospodove, kakor je povedal: "Janez sicer je krstil z vodo, ali vi se boste krstili z Duhom svetim."
17 To, in Allah ya ba su kyauta yadda ya ba mu, mu da muka gaskata da Ubangiji Yesu Kiristi, wane ni da zan yi hamayya da Allah?”
Ko jim je torej Bog dal ravno ta dar, kakor tudi nam, kteri smo verovali v Gospoda Jezusa Kristusa: kdo pa sem bil jaz, da bi bil mogel Bogu zabraniti?
18 Sa’ad da suka ji haka, ba su ƙara yin faɗa ba, suka kuma ɗaukaka Allah, suna cewa, “To, fa, har Al’ummai ma Allah ya sa suka tuba zuwa rai.”
Ko so pa to slišali, umolknili so, in slavili so Boga, govoreč: Torej tudi poganom je Bog dal pokoro za življenje.
19 To, waɗanda suka warwatsu saboda tsananin da ya tashi a kan batun Istifanus suka tafi har Funisiya, Saifurus da kuma Antiyok, suna ba da saƙon ga Yahudawa kaɗai.
Ti pa, kteri so se bili razkropili za voljo stiske, ktera je nastala za Štefana, prišli so noter do Fenicije, nikomur ne govoreč besede, razen samo Judom.
20 Amma waɗansunsu kuwa, mutane daga Saifurus da Sairin, suka je Antiyok suka fara yi wa Hellenawa magana su ma, suna ba da labari mai daɗi game da Ubangiji Yesu.
Bili so pa nekteri od njih možjé Ciprani in Cirenci, kteri so, ko so bili prišli v Antijohijo, govorili tudi Grkom, in oznanjevali Gospoda Jezusa.
21 Hannun Ubangiji kuwa yana tare da su, mutane da yawan gaske kuwa suka gaskata suka juya ga Ubangiji.
In bila je roka Gospodova ž njimi; in veliko število jih je verovalo in izpreobrnilo se h Gospodu.
22 Labari wannan abu ya kai kunnuwan ikkilisiya a Urushalima, sai suka aiki Barnabas zuwa Antiyok.
In prišel je glas o tem do ušes cerkve, ktera je bila v Jeruzalemu; in poslali so Barnaba, naj odide do Antijohije.
23 Da ya iso ya kuma ga tabbacin alherin Allah, sai ya yi farin ciki ya kuma ƙarfafa su duka su tsaya da gaskiya cikin Ubangiji da dukan zukatansu.
Ta, ko je prišel, in je videl milost Božjo, oveselil se je, in prosil je vse, naj s stanovitnim srcem ostanejo v Gospodu.
24 Mutum ne nagari, cike da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya, mutane masu yawan gaske kuwa suka juya ga Ubangiji.
Kajti bil je mož dober in poln Duha svetega in vere. In pridružilo se je veliko ljudstva Gospodu.
25 Sa’an nan Barnabas ya tafi Tarshish don yă nemi Shawulu,
Tedaj izide Barnaba v Tars iskat Savla; in ko ga je našel, pripelje ga v Antijohijo.
26 sa’ad da ya same shi kuwa, sai ya kawo shi Antiyok. Ta haka shekara guda cur Barnabas da Shawulu suka yi suna taruwa da ikkilisiya, suka kuma koya wa mutane masu yawan gaske. A Antiyok ne aka fara kiran almajirai da suna Kirista.
In zbirala sta se celo leto v cerkvi, in učila sta dosti ljudstva, in imenovali so se učenci najprej v Antijohiji Kristjani.
27 A wannan lokaci waɗansu annabawa sun zo Antiyok daga Urushalima.
V te dní so pa prišli iz Jeruzalema preroki v Antijohijo.
28 Ɗaya daga cikinsu mai suna Agabus, ya miƙe tsaye ya yi annabci ta wurin Ruhu cewa za a yi yunwa mai tsanani wadda za tă bazu a dukan duniyar Romawa (Wannan ya faru a zamanin mulkin Kalaudiyus.)
In vstavši eden od njih po imenu Agab, oznani po Duhu, da bo lakota velika po vsem svetu; ktera je tudi bila za Klavdija cesarja.
29 Kowanne a cikin almajiran, gwargwadon azancinsa, ya yanke shawara ya ba da gudummawa ga’yan’uwan da suke zama a Yahudiya.
Tedaj učenci, vsak po zmožnosti svojej, sklenejo v pomoč poslati bratom, kteri so prebivali v Judeji;
30 Haka kuwa suka yi, suka aika da kyautarsa wa dattawan ikkilisiyar ta hannu Barnabas da Shawulu.
Kar so tudi storili, poslavši starešinam po roki Barnabovej in Savlovej.