< Ayyukan Manzanni 11 >

1 Manzanni da’yan’uwa ko’ina a Yahudiya suka ji cewa Al’ummai ma sun karɓi maganar Allah.
Or les apôtres et les frères qui étaient en Judée apprirent que les nations aussi avaient reçu la parole de Dieu.
2 Saboda haka sa’ad da Bitrus ya haura zuwa Urushalima, masu bin da suke da kaciya suka zarge shi
Et quand Pierre fut monté à Jérusalem, ceux de la circoncision disputaient avec lui,
3 suka ce, “Ka je gidan mutanen da suke marasa kaciya ka kuwa ci tare da su.”
disant: Tu es entré chez des hommes incirconcis, et tu as mangé avec eux.
4 Bitrus ya fara yin musu bayani dalla-dalla yadda ya faru cewa,
Mais Pierre se mit à leur exposer [les choses] par ordre, disant:
5 “Ina a birnin Yoffa ina addu’a, sai ga wahayi ya zo mini. Na ga ana sauko da wani abu kamar babban mayafi daga sama ta kusurwansa huɗu, ya kuma sauko inda nake.
J’étais en prière dans la ville de Joppé, et je vis dans une extase une vision, [savoir] un vase descendant comme une grande toile dévalée du ciel par les quatre coins; et elle vint jusqu’à moi;
6 Na duba cikinsa na ga dabbobi masu ƙafa huɗu na duniya, da namun jeji, da masu ja da ciki, da kuma tsuntsayen sararin sama.
et y ayant jeté les yeux, je considérais, et je vis les quadrupèdes de la terre, et les bêtes sauvages, et les reptiles, et les oiseaux du ciel;
7 Sa’an nan na ji wata murya tana ce mini, ‘Bitrus, ka tashi. Ka yanka ka ci.’
et j’entendis aussi une voix qui me dit: Lève-toi, Pierre, tue et mange.
8 “Na amsa na ce, ‘Sam, Ubangiji! Ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko marar tsabta ba.’
Et je dis: Non point, Seigneur; car jamais chose impure ou immonde n’entra dans ma bouche.
9 “Sai muryar daga sama ta yi magana sau na biyu, ta ce, ‘Kada ka ce da abin da Allah ya tsarkake marar tsarki.’
Et une voix répondit pour la seconde fois du ciel: Ce que Dieu a purifié, toi, ne le tiens pas pour impur.
10 Wannan ya faru har sau uku, sa’an nan duk aka sāke ɗauke shi zuwa sama.
Et cela eut lieu par trois fois, et tout fut de nouveau retiré dans le ciel.
11 “Nan take sai ga mutum uku da aka aika wurina daga Kaisariya a tsaye a ƙofar gidan da nake.
Et voici, aussitôt, trois hommes qui avaient été envoyés de Césarée vers moi, se trouvèrent devant la maison où j’étais.
12 Ruhu ya ce mini kada in yi wata-wata game da tafiya tare da su. Waɗannan’yan’uwa guda shida su ma suka rako ni, muka kuwa shiga gidan mutumin.
Et l’Esprit me dit d’aller avec eux sans hésiter; et les six frères que voici vinrent avec moi, et nous sommes entrés dans la maison de cet homme.
13 Ya kuma gaya mana yadda wani mala’ika ya bayyana a gidansa ya ce masa, ‘Ka aika zuwa Yoffa a kira Siman wanda ake ce da shi Bitrus.
Et il nous raconta comment il avait vu dans sa maison l’ange qui, se tenant là, lui avait dit: Envoie à Joppé, et fais venir Simon qui est surnommé Pierre,
14 Zai kawo maka saƙo wanda ta wurinsa kai da dukan iyalinka za ku sami ceto.’
qui te dira des choses par lesquelles tu seras sauvé, toi et toute ta maison.
15 “Na fara magana ke nan, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu yadda ya sauko mana a farko.
Et comme je commençais à parler, l’Esprit Saint tomba sur eux, comme aussi [il est tombé] sur nous au commencement.
16 Sa’an nan na tuna da abin da Ubangiji ya ce, ‘Yohanna ya yi baftisma da ruwa, amma za a yi muku baftisma daRuhu Mai Tsarki.’
Et je me souvins de la parole du Seigneur, comment il a dit: Jean a baptisé avec de l’eau, mais vous, vous serez baptisés de l’Esprit Saint.
17 To, in Allah ya ba su kyauta yadda ya ba mu, mu da muka gaskata da Ubangiji Yesu Kiristi, wane ni da zan yi hamayya da Allah?”
Si donc Dieu leur a fait le même don qu’à nous qui avons cru au seigneur Jésus Christ, qui étais-je, moi, pour pouvoir l’interdire à Dieu?
18 Sa’ad da suka ji haka, ba su ƙara yin faɗa ba, suka kuma ɗaukaka Allah, suna cewa, “To, fa, har Al’ummai ma Allah ya sa suka tuba zuwa rai.”
Et ayant entendu ces choses, ils se turent, et glorifièrent Dieu disant: Dieu a donc en effet donné aux nations la repentance pour la vie!
19 To, waɗanda suka warwatsu saboda tsananin da ya tashi a kan batun Istifanus suka tafi har Funisiya, Saifurus da kuma Antiyok, suna ba da saƙon ga Yahudawa kaɗai.
Ceux donc qui avaient été dispersés par la tribulation qui arriva à l’occasion d’Étienne, passèrent jusqu’en Phénicie, et à Chypre, et à Antioche, n’annonçant la parole à personne, si ce n’est à des Juifs seulement.
20 Amma waɗansunsu kuwa, mutane daga Saifurus da Sairin, suka je Antiyok suka fara yi wa Hellenawa magana su ma, suna ba da labari mai daɗi game da Ubangiji Yesu.
Mais quelques-uns d’entre eux étaient des Cypriotes et des Cyrénéens, qui, étant venus à Antioche, parlaient aussi aux Grecs, annonçant le seigneur Jésus;
21 Hannun Ubangiji kuwa yana tare da su, mutane da yawan gaske kuwa suka gaskata suka juya ga Ubangiji.
et la main du Seigneur était avec eux; et un grand nombre, ayant cru, se tournèrent vers le Seigneur.
22 Labari wannan abu ya kai kunnuwan ikkilisiya a Urushalima, sai suka aiki Barnabas zuwa Antiyok.
Et le bruit en vint aux oreilles de l’assemblée qui était à Jérusalem; et ils envoyèrent Barnabas pour passer jusqu’à Antioche;
23 Da ya iso ya kuma ga tabbacin alherin Allah, sai ya yi farin ciki ya kuma ƙarfafa su duka su tsaya da gaskiya cikin Ubangiji da dukan zukatansu.
lequel, y étant arrivé et ayant vu la grâce de Dieu, se réjouit; et il les exhortait tous à demeurer [attachés] au Seigneur de tout leur cœur,
24 Mutum ne nagari, cike da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya, mutane masu yawan gaske kuwa suka juya ga Ubangiji.
car il était homme de bien et plein de l’Esprit Saint et de foi; et une grande foule fut ajoutée au Seigneur.
25 Sa’an nan Barnabas ya tafi Tarshish don yă nemi Shawulu,
Et il s’en alla à Tarse, pour chercher Saul;
26 sa’ad da ya same shi kuwa, sai ya kawo shi Antiyok. Ta haka shekara guda cur Barnabas da Shawulu suka yi suna taruwa da ikkilisiya, suka kuma koya wa mutane masu yawan gaske. A Antiyok ne aka fara kiran almajirai da suna Kirista.
et l’ayant trouvé, il le mena à Antioche. Et il leur arriva que, pendant un an tout entier, ils se réunirent dans l’assemblée et enseignèrent une grande foule, – et que ce fut à Antioche premièrement que les disciples furent nommés chrétiens.
27 A wannan lokaci waɗansu annabawa sun zo Antiyok daga Urushalima.
Or en ces jours-là, des prophètes descendirent de Jérusalem à Antioche.
28 Ɗaya daga cikinsu mai suna Agabus, ya miƙe tsaye ya yi annabci ta wurin Ruhu cewa za a yi yunwa mai tsanani wadda za tă bazu a dukan duniyar Romawa (Wannan ya faru a zamanin mulkin Kalaudiyus.)
Et l’un d’entre eux, nommé Agabus, se leva et déclara par l’Esprit, qu’une grande famine aurait lieu dans toute la terre habitée, laquelle aussi eut lieu sous Claude.
29 Kowanne a cikin almajiran, gwargwadon azancinsa, ya yanke shawara ya ba da gudummawa ga’yan’uwan da suke zama a Yahudiya.
Et les disciples, chacun selon ses ressources, déterminèrent d’envoyer quelque chose pour le service des frères qui demeuraient en Judée:
30 Haka kuwa suka yi, suka aika da kyautarsa wa dattawan ikkilisiyar ta hannu Barnabas da Shawulu.
ce qu’ils firent aussi, l’envoyant aux anciens par les mains de Barnabas et de Saul.

< Ayyukan Manzanni 11 >