< Ayyukan Manzanni 11 >

1 Manzanni da’yan’uwa ko’ina a Yahudiya suka ji cewa Al’ummai ma sun karɓi maganar Allah.
And the apostles and the brethren who are in Judea heard that also the nations did receive the word of God,
2 Saboda haka sa’ad da Bitrus ya haura zuwa Urushalima, masu bin da suke da kaciya suka zarge shi
and when Peter came up to Jerusalem, those of the circumcision were contending with him,
3 suka ce, “Ka je gidan mutanen da suke marasa kaciya ka kuwa ci tare da su.”
saying — 'Unto men uncircumcised thou didst go in, and didst eat with them!'
4 Bitrus ya fara yin musu bayani dalla-dalla yadda ya faru cewa,
And Peter having begun, did expound to them in order saying,
5 “Ina a birnin Yoffa ina addu’a, sai ga wahayi ya zo mini. Na ga ana sauko da wani abu kamar babban mayafi daga sama ta kusurwansa huɗu, ya kuma sauko inda nake.
'I was in the city of Joppa praying, and I saw in a trance a vision, a certain vessel coming down, as a great sheet by four corners being let down out of the heaven, and it came unto me;
6 Na duba cikinsa na ga dabbobi masu ƙafa huɗu na duniya, da namun jeji, da masu ja da ciki, da kuma tsuntsayen sararin sama.
at which having looked stedfastly, I was considering, and I saw the four-footed beasts of the earth, and the wild beasts, and the creeping things, and the fowls of heaven;
7 Sa’an nan na ji wata murya tana ce mini, ‘Bitrus, ka tashi. Ka yanka ka ci.’
and I heard a voice saying to me, Having risen, Peter, slay and eat;
8 “Na amsa na ce, ‘Sam, Ubangiji! Ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko marar tsabta ba.’
and I said, Not so, Lord; because anything common or unclean hath at no time entered into my mouth;
9 “Sai muryar daga sama ta yi magana sau na biyu, ta ce, ‘Kada ka ce da abin da Allah ya tsarkake marar tsarki.’
and a voice did answer me a second time out of the heaven, What God did cleanse, thou — declare not thou common.
10 Wannan ya faru har sau uku, sa’an nan duk aka sāke ɗauke shi zuwa sama.
'And this happened thrice, and again was all drawn up to the heaven,
11 “Nan take sai ga mutum uku da aka aika wurina daga Kaisariya a tsaye a ƙofar gidan da nake.
and, lo, immediately, three men stood at the house in which I was, having been sent from Caesarea unto me,
12 Ruhu ya ce mini kada in yi wata-wata game da tafiya tare da su. Waɗannan’yan’uwa guda shida su ma suka rako ni, muka kuwa shiga gidan mutumin.
and the Spirit said to me to go with them, nothing doubting, and these six brethren also went with me, and we did enter into the house of the man,
13 Ya kuma gaya mana yadda wani mala’ika ya bayyana a gidansa ya ce masa, ‘Ka aika zuwa Yoffa a kira Siman wanda ake ce da shi Bitrus.
he declared also to us how he saw the messenger in his house standing, and saying to him, Send men to Joppa, and call for Simon, who is surnamed Peter,
14 Zai kawo maka saƙo wanda ta wurinsa kai da dukan iyalinka za ku sami ceto.’
who shall speak sayings by which thou shalt be saved, thou and all thy house.
15 “Na fara magana ke nan, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu yadda ya sauko mana a farko.
'And in my beginning to speak, the Holy Spirit did fall upon them, even as also upon us in the beginning,
16 Sa’an nan na tuna da abin da Ubangiji ya ce, ‘Yohanna ya yi baftisma da ruwa, amma za a yi muku baftisma daRuhu Mai Tsarki.’
and I remembered the saying of the Lord, how he said, John indeed did baptize with water, and ye shall be baptized with the Holy Spirit;
17 To, in Allah ya ba su kyauta yadda ya ba mu, mu da muka gaskata da Ubangiji Yesu Kiristi, wane ni da zan yi hamayya da Allah?”
if then the equal gift God did give to them as also to us, having believed upon the Lord Jesus Christ, I — how was I able to withstand God?'
18 Sa’ad da suka ji haka, ba su ƙara yin faɗa ba, suka kuma ɗaukaka Allah, suna cewa, “To, fa, har Al’ummai ma Allah ya sa suka tuba zuwa rai.”
And they, having heard these things, were silent, and were glorifying God, saying, 'Then, indeed, also to the nations did God give the reformation to life.'
19 To, waɗanda suka warwatsu saboda tsananin da ya tashi a kan batun Istifanus suka tafi har Funisiya, Saifurus da kuma Antiyok, suna ba da saƙon ga Yahudawa kaɗai.
Those, indeed, therefore, having been scattered abroad, from the tribulation that came after Stephen, went through unto Phenice, and Cyprus, and Antioch, speaking the word to none except to Jews only;
20 Amma waɗansunsu kuwa, mutane daga Saifurus da Sairin, suka je Antiyok suka fara yi wa Hellenawa magana su ma, suna ba da labari mai daɗi game da Ubangiji Yesu.
and there were certain of them men of Cyprus and Cyrene, who having entered into Antioch, were speaking unto the Hellenists, proclaiming good news — the Lord Jesus,
21 Hannun Ubangiji kuwa yana tare da su, mutane da yawan gaske kuwa suka gaskata suka juya ga Ubangiji.
and the hand of the Lord was with them, a great number also, having believed, did turn unto the Lord.
22 Labari wannan abu ya kai kunnuwan ikkilisiya a Urushalima, sai suka aiki Barnabas zuwa Antiyok.
And the account was heard in the ears of the assembly that [is] in Jerusalem concerning them, and they sent forth Barnabas to go through unto Antioch,
23 Da ya iso ya kuma ga tabbacin alherin Allah, sai ya yi farin ciki ya kuma ƙarfafa su duka su tsaya da gaskiya cikin Ubangiji da dukan zukatansu.
who, having come, and having seen the grace of God, was glad, and was exhorting all with purpose of heart to cleave to the Lord,
24 Mutum ne nagari, cike da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya, mutane masu yawan gaske kuwa suka juya ga Ubangiji.
because he was a good man, and full of the Holy Spirit, and of faith, and a great multitude was added to the Lord.
25 Sa’an nan Barnabas ya tafi Tarshish don yă nemi Shawulu,
And Barnabas went forth to Tarsus, to seek for Saul,
26 sa’ad da ya same shi kuwa, sai ya kawo shi Antiyok. Ta haka shekara guda cur Barnabas da Shawulu suka yi suna taruwa da ikkilisiya, suka kuma koya wa mutane masu yawan gaske. A Antiyok ne aka fara kiran almajirai da suna Kirista.
and having found him, he brought him to Antioch, and it came to pass that they a whole year did assemble together in the assembly, and taught a great multitude, the disciples also were divinely called first in Antioch Christians.
27 A wannan lokaci waɗansu annabawa sun zo Antiyok daga Urushalima.
And in those days there came from Jerusalem prophets to Antioch,
28 Ɗaya daga cikinsu mai suna Agabus, ya miƙe tsaye ya yi annabci ta wurin Ruhu cewa za a yi yunwa mai tsanani wadda za tă bazu a dukan duniyar Romawa (Wannan ya faru a zamanin mulkin Kalaudiyus.)
and one of them, by name Agabus, having stood up, did signify through the Spirit a great dearth is about to be throughout all the world — which also came to pass in the time of Claudius Caesar —
29 Kowanne a cikin almajiran, gwargwadon azancinsa, ya yanke shawara ya ba da gudummawa ga’yan’uwan da suke zama a Yahudiya.
and the disciples, according as any one was prospering, determined each of them to send for ministration to the brethren dwelling in Judea,
30 Haka kuwa suka yi, suka aika da kyautarsa wa dattawan ikkilisiyar ta hannu Barnabas da Shawulu.
which also they did, having sent unto the elders by the hand of Barnabas and Saul.

< Ayyukan Manzanni 11 >