< Ayyukan Manzanni 11 >

1 Manzanni da’yan’uwa ko’ina a Yahudiya suka ji cewa Al’ummai ma sun karɓi maganar Allah.
And the apostles and brethren that were in Judea, heard that the Gentiles also had received the word of God.
2 Saboda haka sa’ad da Bitrus ya haura zuwa Urushalima, masu bin da suke da kaciya suka zarge shi
And when Peter had come to Jerusalem, they that were of the circumcision contended with him,
3 suka ce, “Ka je gidan mutanen da suke marasa kaciya ka kuwa ci tare da su.”
Saying, Thou wentest in to men uncircumcised, and didst eat with them.
4 Bitrus ya fara yin musu bayani dalla-dalla yadda ya faru cewa,
But Peter rehearsed [the matter] from the beginning, and expounded [it] by order to them, saying,
5 “Ina a birnin Yoffa ina addu’a, sai ga wahayi ya zo mini. Na ga ana sauko da wani abu kamar babban mayafi daga sama ta kusurwansa huɗu, ya kuma sauko inda nake.
I was in the city of Joppa praying: and in a trance I saw a vision, A certain vessel descend, as it had been a great sheet, let down from heaven by four corners; and it came even to me:
6 Na duba cikinsa na ga dabbobi masu ƙafa huɗu na duniya, da namun jeji, da masu ja da ciki, da kuma tsuntsayen sararin sama.
Upon which when I had fastened my eyes, I considered, and saw four-footed beasts of the earth, and wild beasts, and creeping animals, and fowls of the air.
7 Sa’an nan na ji wata murya tana ce mini, ‘Bitrus, ka tashi. Ka yanka ka ci.’
And I heard a voice saying to me, Arise, Peter; slay and eat.
8 “Na amsa na ce, ‘Sam, Ubangiji! Ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko marar tsabta ba.’
But I said, Not so, Lord: for nothing common or unclean hath at any time entered into my mouth.
9 “Sai muryar daga sama ta yi magana sau na biyu, ta ce, ‘Kada ka ce da abin da Allah ya tsarkake marar tsarki.’
But the voice answered me again from heaven, What God hath cleansed, [that] call not thou common.
10 Wannan ya faru har sau uku, sa’an nan duk aka sāke ɗauke shi zuwa sama.
And this was done three times: and all were drawn up again into heaven.
11 “Nan take sai ga mutum uku da aka aika wurina daga Kaisariya a tsaye a ƙofar gidan da nake.
And behold, immediately there were three men already come to the house where I was, sent from Cesarea to me.
12 Ruhu ya ce mini kada in yi wata-wata game da tafiya tare da su. Waɗannan’yan’uwa guda shida su ma suka rako ni, muka kuwa shiga gidan mutumin.
And the Spirit bade me go with them, nothing doubting. Moreover, these six brethren accompanied me, and we entered into the man's house:
13 Ya kuma gaya mana yadda wani mala’ika ya bayyana a gidansa ya ce masa, ‘Ka aika zuwa Yoffa a kira Siman wanda ake ce da shi Bitrus.
And he showed us how he had seen an angel in his house, who stood and said to him, Send men to Joppa, and call for Simon, whose surname is Peter;
14 Zai kawo maka saƙo wanda ta wurinsa kai da dukan iyalinka za ku sami ceto.’
Who shall tell thee words, by which thou and all thy house shall be saved.
15 “Na fara magana ke nan, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu yadda ya sauko mana a farko.
And as I began to speak, the Holy Spirit fell on them, as on us at the beginning.
16 Sa’an nan na tuna da abin da Ubangiji ya ce, ‘Yohanna ya yi baftisma da ruwa, amma za a yi muku baftisma daRuhu Mai Tsarki.’
Then I remembered the word of the Lord, how he said, John indeed baptized with water; but ye shall be baptized with the Holy Spirit.
17 To, in Allah ya ba su kyauta yadda ya ba mu, mu da muka gaskata da Ubangiji Yesu Kiristi, wane ni da zan yi hamayya da Allah?”
Forasmuch then as God gave them the like gift as [he did] to us, who believed on the Lord Jesus Christ, what was I that I could withstand God?
18 Sa’ad da suka ji haka, ba su ƙara yin faɗa ba, suka kuma ɗaukaka Allah, suna cewa, “To, fa, har Al’ummai ma Allah ya sa suka tuba zuwa rai.”
When they heard these things, they held their peace, and glorified God, saying, Then hath God also to the Gentiles granted repentance to life.
19 To, waɗanda suka warwatsu saboda tsananin da ya tashi a kan batun Istifanus suka tafi har Funisiya, Saifurus da kuma Antiyok, suna ba da saƙon ga Yahudawa kaɗai.
Now they who were dispersed upon the persecution that arose about Stephen traveled as far as Phenice, and Cyprus, and Antioch, preaching the word to none but to the Jews only.
20 Amma waɗansunsu kuwa, mutane daga Saifurus da Sairin, suka je Antiyok suka fara yi wa Hellenawa magana su ma, suna ba da labari mai daɗi game da Ubangiji Yesu.
And some of them were men of Cyprus and Cyrene, who when they had come to Antioch, spoke to the Grecians, preaching the Lord Jesus.
21 Hannun Ubangiji kuwa yana tare da su, mutane da yawan gaske kuwa suka gaskata suka juya ga Ubangiji.
And the hand of the Lord was with them: and a great number believed, and turned to the Lord.
22 Labari wannan abu ya kai kunnuwan ikkilisiya a Urushalima, sai suka aiki Barnabas zuwa Antiyok.
Then tidings of these things came to the ears of the church which was in Jerusalem: and they sent forth Barnabas, that he should go as far as Antioch.
23 Da ya iso ya kuma ga tabbacin alherin Allah, sai ya yi farin ciki ya kuma ƙarfafa su duka su tsaya da gaskiya cikin Ubangiji da dukan zukatansu.
Who, when he came, and had seen the grace of God, was glad, and exhorted them all that with purpose of heart they would cleave to the Lord.
24 Mutum ne nagari, cike da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya, mutane masu yawan gaske kuwa suka juya ga Ubangiji.
For he was a good man, and full of the Holy Spirit, and of faith: and many people were added to the Lord.
25 Sa’an nan Barnabas ya tafi Tarshish don yă nemi Shawulu,
Then Barnabas departed to Tarsus, to seek Saul:
26 sa’ad da ya same shi kuwa, sai ya kawo shi Antiyok. Ta haka shekara guda cur Barnabas da Shawulu suka yi suna taruwa da ikkilisiya, suka kuma koya wa mutane masu yawan gaske. A Antiyok ne aka fara kiran almajirai da suna Kirista.
And when he had found him, he brought him to Antioch. And it came to pass, that a whole year they assembled themselves with the church, and taught many people. And the disciples were first called Christians in Antioch.
27 A wannan lokaci waɗansu annabawa sun zo Antiyok daga Urushalima.
And in these days came prophets from Jerusalem to Antioch.
28 Ɗaya daga cikinsu mai suna Agabus, ya miƙe tsaye ya yi annabci ta wurin Ruhu cewa za a yi yunwa mai tsanani wadda za tă bazu a dukan duniyar Romawa (Wannan ya faru a zamanin mulkin Kalaudiyus.)
And there stood up one of them named Agabus, and signified by the Spirit that there should be great dearth throughout all the world: which came to pass in the days of Claudius Cesar.
29 Kowanne a cikin almajiran, gwargwadon azancinsa, ya yanke shawara ya ba da gudummawa ga’yan’uwan da suke zama a Yahudiya.
Then the disciples, every man according to his ability, determined to send relief to the brethren who dwelt in Judea.
30 Haka kuwa suka yi, suka aika da kyautarsa wa dattawan ikkilisiyar ta hannu Barnabas da Shawulu.
Which also they did, and sent it to the elders by the hands of Barnabas and Saul.

< Ayyukan Manzanni 11 >