< Ayyukan Manzanni 11 >
1 Manzanni da’yan’uwa ko’ina a Yahudiya suka ji cewa Al’ummai ma sun karɓi maganar Allah.
Apoštolové a ti bratři, kteří zůstali v Judsku, se dozvěděli, že i pohané uvěřili Boží zvěsti.
2 Saboda haka sa’ad da Bitrus ya haura zuwa Urushalima, masu bin da suke da kaciya suka zarge shi
Když se Petr vrátil do Jeruzaléma, někteří křesťané židovského původu mu vyčítali:
3 suka ce, “Ka je gidan mutanen da suke marasa kaciya ka kuwa ci tare da su.”
„Ty jsi navštěvoval pohany a dokonce jsi s nimi jedl!“
4 Bitrus ya fara yin musu bayani dalla-dalla yadda ya faru cewa,
Petr jim to pěkně po pořádku vypověděl.
5 “Ina a birnin Yoffa ina addu’a, sai ga wahayi ya zo mini. Na ga ana sauko da wani abu kamar babban mayafi daga sama ta kusurwansa huɗu, ya kuma sauko inda nake.
Vyprávěl o vidění, které měl na střeše domu v Joppe, o příchodu Kornéliových poslů a o všem, co se pak událo v Césareji. Představil jim i šest křesťanů z Joppe, kteří s ním šli ke Kornéliovi. Pak Petr ukončil slovy:
6 Na duba cikinsa na ga dabbobi masu ƙafa huɗu na duniya, da namun jeji, da masu ja da ciki, da kuma tsuntsayen sararin sama.
7 Sa’an nan na ji wata murya tana ce mini, ‘Bitrus, ka tashi. Ka yanka ka ci.’
8 “Na amsa na ce, ‘Sam, Ubangiji! Ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko marar tsabta ba.’
9 “Sai muryar daga sama ta yi magana sau na biyu, ta ce, ‘Kada ka ce da abin da Allah ya tsarkake marar tsarki.’
10 Wannan ya faru har sau uku, sa’an nan duk aka sāke ɗauke shi zuwa sama.
11 “Nan take sai ga mutum uku da aka aika wurina daga Kaisariya a tsaye a ƙofar gidan da nake.
12 Ruhu ya ce mini kada in yi wata-wata game da tafiya tare da su. Waɗannan’yan’uwa guda shida su ma suka rako ni, muka kuwa shiga gidan mutumin.
13 Ya kuma gaya mana yadda wani mala’ika ya bayyana a gidansa ya ce masa, ‘Ka aika zuwa Yoffa a kira Siman wanda ake ce da shi Bitrus.
14 Zai kawo maka saƙo wanda ta wurinsa kai da dukan iyalinka za ku sami ceto.’
15 “Na fara magana ke nan, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu yadda ya sauko mana a farko.
„Když jsem k nim mluvil o Kristu, sestoupil na ně svatý Duch právě tak jako tenkrát na nás.
16 Sa’an nan na tuna da abin da Ubangiji ya ce, ‘Yohanna ya yi baftisma da ruwa, amma za a yi muku baftisma daRuhu Mai Tsarki.’
Vzpomněl jsem si v té chvíli na slova Pána Ježíše: ‚Jan vás křtil na znamení pokání vodou, ale vy budete pokřtěni svatým Duchem.‘
17 To, in Allah ya ba su kyauta yadda ya ba mu, mu da muka gaskata da Ubangiji Yesu Kiristi, wane ni da zan yi hamayya da Allah?”
A tak když uvěřili v Pána Ježíše Krista jako my a dostali i stejný dar od Boha, nemohl jsem se přece stavět proti Boží vůli!“
18 Sa’ad da suka ji haka, ba su ƙara yin faɗa ba, suka kuma ɗaukaka Allah, suna cewa, “To, fa, har Al’ummai ma Allah ya sa suka tuba zuwa rai.”
Když to židovští bratři vyslechli, uklidnili se, s radostí děkovali Bohu a říkali: „Tedy i pohany probouzí Bůh k pokání a k novému životu!“
19 To, waɗanda suka warwatsu saboda tsananin da ya tashi a kan batun Istifanus suka tafi har Funisiya, Saifurus da kuma Antiyok, suna ba da saƙon ga Yahudawa kaɗai.
Ti věřící, kteří po Štěpánově smrti při pronásledování uprchli z Jeruzaléma, se dostali až do Fénicie, na Kypr a do města Antiochie v Sýrii. Radostné zvěsti o spáse hlásali jenom židům.
20 Amma waɗansunsu kuwa, mutane daga Saifurus da Sairin, suka je Antiyok suka fara yi wa Hellenawa magana su ma, suna ba da labari mai daɗi game da Ubangiji Yesu.
Někteří však, rodáci z Kypru a Kyrenaiky, začali v Antiochii mluvit o Ježíši Kristu také pohanům.
21 Hannun Ubangiji kuwa yana tare da su, mutane da yawan gaske kuwa suka gaskata suka juya ga Ubangiji.
Pán stál při nich a velký počet lidí uvěřil a obrátil se ke Kristu.
22 Labari wannan abu ya kai kunnuwan ikkilisiya a Urushalima, sai suka aiki Barnabas zuwa Antiyok.
Když se o tom doslechli v jeruzalémském sboru, vyslali do Antiochie Barnabáše.
23 Da ya iso ya kuma ga tabbacin alherin Allah, sai ya yi farin ciki ya kuma ƙarfafa su duka su tsaya da gaskiya cikin Ubangiji da dukan zukatansu.
Ten tam uviděl, jak mocně zapůsobila Boží milost. Měl z toho velkou radost a všechny povzbuzoval, aby věrně vytrvali při svém rozhodnutí pro Pána.
24 Mutum ne nagari, cike da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya, mutane masu yawan gaske kuwa suka juya ga Ubangiji.
Barnabáš byl muž na svém místě, plný Ducha svatého a víry. V Antiochii bylo pro Ježíše získáno velké množství pohanů.
25 Sa’an nan Barnabas ya tafi Tarshish don yă nemi Shawulu,
Barnabáš se odtud vypravil do Tarsu, vyhledal Saula a přivedl ho s sebou do Antiochie.
26 sa’ad da ya same shi kuwa, sai ya kawo shi Antiyok. Ta haka shekara guda cur Barnabas da Shawulu suka yi suna taruwa da ikkilisiya, suka kuma koya wa mutane masu yawan gaske. A Antiyok ne aka fara kiran almajirai da suna Kirista.
Tam zůstali po celý rok, a když kázali o Kristu, připojilo se ke skupině tamějších věřících překvapivé množství lidí. V Antiochii se poprvé začalo říkat Kristovým následovníkům kristovci – křesťané.
27 A wannan lokaci waɗansu annabawa sun zo Antiyok daga Urushalima.
Do antiochijského sboru přišli také z Jeruzaléma někteří věřící, kteří měli dar prorockého vidění.
28 Ɗaya daga cikinsu mai suna Agabus, ya miƙe tsaye ya yi annabci ta wurin Ruhu cewa za a yi yunwa mai tsanani wadda za tă bazu a dukan duniyar Romawa (Wannan ya faru a zamanin mulkin Kalaudiyus.)
Jednomu z nich, Agabovi, ukázal Bůh, že v celé říši bude velký hlad. To se skutečně vyplnilo za vlády císaře Klaudia.
29 Kowanne a cikin almajiran, gwargwadon azancinsa, ya yanke shawara ya ba da gudummawa ga’yan’uwan da suke zama a Yahudiya.
Křesťané v Antiochii se tedy rozhodli přispět každý podle svých možností a podpořit věřící v Judsku, kde bylo mnoho chudých.
30 Haka kuwa suka yi, suka aika da kyautarsa wa dattawan ikkilisiyar ta hannu Barnabas da Shawulu.
Sbírku poslali představeným církve v Jeruzalémě po Barnabášovi a Saulovi.