< Ayyukan Manzanni 10 >
1 A Kaisariya akwai wani mutum mai suna Korneliyus, wani jarumin Roma ne, a ƙungiyar soja da ake kira Bataliyar Italiya.
A u Æesariji bješe jedan èovjek po imenu Kornilije, kapetan od èete koja se zvaše Talijanska.
2 Shi da dukan iyalinsa masu ibada ne masu tsoron Allah kuma; yakan ba da kyauta hannu sake ga masu bukata yana kuma addu’a ga Allah ba fasawa.
Pobožan i bogobojazan sa cijelijem domom svojijem, koji davaše milostinju mnogijem ljudima i moljaše se Bogu bez prestanka;
3 Wata rana wajen ƙarfe uku na yamma ya ga wahayi. A sarari ya ga wani mala’ikan Allah, wanda ya zo wajensa ya ce, “Korneliyus!”
On vidje na javi u utvari oko devetoga sahata dnevi anðela Božijega gdje siðe k njemu i reèe mu: Kornilije!
4 Korneliyus kuwa ya zura masa ido a tsorace ya ce, “Mene ne, ya Ubangiji?” Mala’ikan ya ce, “Addu’o’inka da kyautanka ga matalauta sun kai har sama, hadayar tunawa ce a gaban Allah.
A on pogledavši na nj i uplašivši se reèe: što je Gospode? A on mu reèe: molitve tvoje i milostinje iziðoše na pamet Bogu;
5 Yanzu sai ka aiki mutane zuwa Yoffa su dawo da wani mutum mai suna Siman wanda ake kira Bitrus.
I sad pošlji u Jopu ljude i dozovi Simona prozvanoga Petra:
6 Yana zama tare da Siman, mai aikin fatu, wanda gidansa ke bakin teku.”
On stoji u nekoga Simona kožara, kojega je kuæa kod mora: on æe ti kazati rijeèi kojima æeš se spasti ti i sav dom tvoj.
7 Sa’ad da mala’ikan da ya yi masa magana ya tafi, sai Korneliyus ya kira biyu daga cikin bayinsa da kuma wani soja mai ibada wanda yake ɗaya a cikin masu yin masa hidima.
I kad otide anðeo koji govori Korniliju, dozvavši dvojicu od svojijeh slugu i jednoga pobožna vojnika od onijeh koji mu služahu,
8 Ya fada musu duk abin da ya faru sa’an nan ya aike su Yoffa.
I kazavši im sve posla ih u Jopu.
9 Wajen tsakar rana kashegari yayinda suke cikin tafiyarsu suna kuma dab da birnin, sai Bitrus ya hau bisan rufin gida yă yi addu’a.
A sjutradan kad oni iðahu putem i približiše se ka gradu, iziðe Petar u gornju sobu da se pomoli Bogu u šesti sahat.
10 Yunwa ta kama shi ya kuwa so yă ci wani abu, yayinda ake shirya abinci, sai wahayi ya zo masa.
I ogladnje, i šæaše da jede; a kad mu oni gotovljahu, doðe izvan sebe,
11 Ya ga sama ya buɗe ana kuwa saukowa wani abu ƙasa kamar babban mayafi zuwa duniya ta kusurwansa huɗu.
I vidje nebo otvoreno i sud nekakav gdje silazi na njega, kao veliko platno, zavezan na èetiri roglja i spušta se na zemlju;
12 Cikinsa kuwa akwai kowace irin dabba mai ƙafa huɗu da masu ja da ciki na duniya da kuma tsuntsayen sararin sama.
U kome bijahu sva èetvoronožna na zemlji, i zvjerinje i bubine i ptice nebeske.
13 Sa’an nan wata murya ta ce masa, “Bitrus, ka tashi. Ka yanka ka ci.”
I postade glas k njemu: ustani, Petre! pokolji i pojedi.
14 Bitrus ya ce, “Sam, Ubangiji! Ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko marar tsabta ba.”
A Petar reèe: nipošto, Gospode! jer nikad ne jedoh što pogano ili neèisto.
15 Muryar ta yi magana da shi sau na biyu ta ce, “Kada ka ce da abin da Allah ya tsarkake marar tsarki.”
I gle, glas opet k njemu drugom: što je Bog oèistio ti ne pogani.
16 Wannan ya faru har sau uku, sai nan da nan aka ɗauke mayafin zuwa sama.
I ovo bi triput, i sud se opet uze na nebo.
17 Tun Bitrus yana cikin tunani game da ma’anar wahayin nan, sai ga mutanen da Korneliyus ya aika sun sami gidan Siman suna kuma tsaye a ƙofar.
A kad se Petar u sebi divljaše šta bi bila utvara koju vidje, i gle, ljudi poslani od Kornilija, napitavši i našavši dom Simonov stadoše pred vratima,
18 Suka yi sallama, suna tambaya ko Siman wanda aka sani da suna Bitrus yana zama a can.
I zovnuvši pitahu: stoji li ovdje Simon prozvani Petar?
19 Yayinda Bitrus yana cikin tunani game da wahayin, sai Ruhu ya ce masa, “Siman, ga mutum uku suna nemanka.
A dok Petar razmišljavaše o utvari, reèe mu Duh: evo tri èovjeka traže te;
20 Saboda haka ka tashi ka sauka. Kada ka yi wata-wata, gama ni ne na aiko su.”
Nego ustani i siði i idi s njima ne premišljajuæi ništa, jer ih ja poslah.
21 Sai Bitrus ya sauka ya ce wa mutanen, “Ni ne kuke nema. Me ya kawo ku?”
A Petar sišavši k ljudima poslanijem k sebi od Kornilija reèe: evo ja sam koga tražite; što ste došli?
22 Mutanen suka amsa, “Mun zo ne daga wurin Korneliyus wani jarumin. Shi mutum ne mai adalci mai tsoron Allah kuma, wanda dukan Yahudawa ke girmamawa. Wani mala’ika mai tsarki ya faɗa masa, yă sa ka zo gidansa don yă ji abin da za ka faɗa.”
A oni rekoše: Kornilije kapetan, èovjek pravedan i bogobojazan, poznat kod svega naroda Jevrejskoga, primio je zapovijest od anðela svetoga da dozove tebe u svoj dom i da èuje rijeèi od tebe.
23 Sai Bitrus ya gayyaci mutanen cikin gida su zama baƙinsa. Kashegari Bitrus ya tafi tare da su, waɗansu’yan’uwa daga Yoffa kuwa suka tafi tare da shi.
Onda ih dozva unutra i ugosti. A sjutradan ustavši Petar poðe s njima, i neki od braæe koja bješe u Jopi poðoše s njim.
24 Kashegari sai ya iso Kaisariya. Korneliyus kuwa yana nan yana jiransu, ya kuma gayyaci’yan’uwansa da abokansa na kusa.
I sjutradan uðoše u Æesariju. A Kornilije èekaše ih sazvavši rodbinu svoju i ljubazne prijatelje.
25 Da Bitrus ya shiga gidan, Korneliyus ya sadu da shi ya kuma fāɗi a gabansa cikin bangirma.
A kad Petar šæaše da uðe, srete ga Kornilije, i padnuvši na noge njegove pokloni se.
26 Amma Bitrus ya sa shi ya tashi. Ya ce, “Tashi, ni mutum ne kawai.”
I Petar ga podiže govoreæi: ustani, i ja sam èovjek.
27 Yana magana da shi, sai Bitrus ya shiga ciki ya kuma tarar da taron mutane da yawa.
I s njim govoreæi uðe, i naðe mnoge koji se bijahu sabrali.
28 Sai ya ce musu, “Ku da kanku kun san cewa dokarmu ta hana mutumin Yahuda yin cuɗanya, ko ya ziyarci Ba’al’umme. Amma Allah ya nuna mini cewa kada in kira wani mutum marar tsarki ko marar tsabta.
I reèe im: vi znate kako je neprilièno èovjeku Jevrejinu družiti se ili dolaziti k tuðinu; ali Bog meni pokaza da nijednoga èovjeka ne zovem pogana ili neèista;
29 Don haka sa’ad da aka aika in zo, na zo ba wata faɗa. To, ko zan san abin da ya sa ka aika in zo?”
Zato i bez sumnje doðoh pozvan. Pitam vas dakle zašto poslaste po mene?
30 Korneliyus ya amsa ya ce, “Kwana huɗu da suka wuce ina a gidana ina addu’a a wannan lokaci, wajen ƙarfe uku na yamma. Ba zato ba tsammani sai ga wani mutum cikin tufafi masu walƙiya ya tsaya a gabana
I Kornilije reèe: od èetvrtoga dana do ovoga èasa ja postih, i u deveti sahat moljah se Bogu u svojoj kuæi; i gle, èovjek stade preda mnom u haljini sjajnoj,
31 ya ce, ‘Korneliyus, Allah ya ji addu’arka, ya kuma tuna da kyautanka ga matalauta.
I reèe: Kornilije! uslišena bi molitva tvoja i milostinje tvoje pomenuše se pred Bogom.
32 Ka aika zuwa Yoffa don a kira Siman wanda ake ce da shi Bitrus. Shi baƙo ne a gidan Siman mai aikin fatu, wanda yake zama a bakin teku.’
Pošlji dakle u Jopu i dozovi Simona koji se zove Petar: on stoji u kuæi Simona kožara kod mora, koji kad doðe kazaæe ti.
33 Saboda haka na aika a zo da kai nan da nan, ya kuma yi kyau da ka zo. To ga mu duka a nan a gaban Allah don mu saurari dukan abin da Ubangiji ya umarce ka ka faɗa mana.”
Onda ja odmah poslah k tebi; i ti si dobro uèinio što si došao. Sad dakle mi svi stojimo pred Bogom da èujemo sve što je tebi od Boga zapovjeðeno.
34 Sa’an nan Bitrus ya fara magana ya ce, “Yanzu na gane yadda gaskiya ne cewa Allah ba ya sonkai
A Petar otvorivši usta reèe: zaista vidim da Bog ne gleda ko je ko;
35 amma yana karɓan mutane daga kowace al’ummar da take tsoronsa suke kuma aikata abin da yake daidai.
Nego u svakom narodu koji se boji njega i tvori pravdu mio je njemu.
36 Kun san saƙon da Allah ya aika wa mutanen Isra’ila, yana shelar labari mai daɗi na salama ta wurin Yesu Kiristi, shi ne kuwa Ubangijin kowa.
Rijeè što posla sinovima Izrailjevijem, javljajuæi mir po Isusu Hristu, ona je Gospod svima.
37 Kun san abin da ya faru a dukan Yahudiya, farawa daga Galili bayan baftismar da Yohanna ya yi wa’azi,
Vi znate govor koji je bio po svoj Judeji poèevši od Galileje po krštenju koje propovijeda Jovan:
38 yadda Allah ya shafe Yesu Banazare da Ruhu Mai Tsarki da kuma iko, da kuma yadda ya zaga ko’ina yana aikata alheri yana kuma warkar da dukan waɗanda suke ƙarƙashin ikon Iblis, domin Allah yana tare da shi.
Isusa iz Nazareta kako ga pomaza Bog Duhom svetijem i silom, koji proðe èineæi dobro i iscjeljujuæi sve koje ðavo bješe nadvladao; jer Bog bijaše s njim.
39 “Mu kuwa shaidu ne na dukan abin da ya yi a ƙasar Yahudawa da kuma a Urushalima. Suka kashe shi ta wurin rataye shi a kan itace,
I mi smo svjedoci svemu što uèini u zemlji Judejskoj i Jerusalimu; kojega i ubiše objesivši na drvo.
40 amma Allah ya tashe shi daga matattu a rana ta uku, ya sa kuma aka gan shi.
Ovoga Bog vaskrse treæi dan, i dade mu da se pokaže,
41 Ba dukan mutane ne suka gan shi ba, amma ta wurin shaidun da Allah ya riga ya zaɓa, ta wurinmu da muka ci muka kuma sha tare da shi bayan tashinsa daga matattu.
Ne svemu narodu nego nama svjedocima naprijed izbranima od Boga, koji s njim jedosmo i pismo po vaskrseniju njegovom iz mrtvijeh.
42 Ya umarce mu mu yi wa’azi ga mutane mu kuma shaida cewa shi ne wanda Allah ya naɗa yă zama mai shari’a na masu rai da na matattu.
I zapovjedi nam da propovijedamo narodu i da svjedoèimo da je on nareèeni od Boga sudija živijem i mrtvijem.
43 Duk annabawa sun yi shaida game da shi cewa duk wanda ya ba da gaskiya gare shi zai sami gafarar zunubai ta wurin sunansa.”
Za ovo svjedoèe svi proroci da æe imenom njegovijem primiti oproštenje grijeha svi koji ga vjeruju.
44 Tun Bitrus yana cikin faɗin waɗannan kalmomi, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauka wa duk waɗanda suka ji saƙon.
A dok još Petar govoraše ove rijeèi, siðe Duh sveti na sve koji slušahu rijeè.
45 Masu bin da suke da kaciya waɗanda suka zo tare da Bitrus suka yi mamaki cewa an ba da kyautar Ruhu Mai Tsarki har ma a kan Al’ummai.
I udiviše se vjerni iz obrezanja koji bijahu došli s Petrom, videæi da se i na neznabošce izli dar Duha svetoga.
46 Gama sun ji su suna magana da waɗansu harsuna suna kuma yabon Allah. Sai Bitrus ya ce,
Jer ih slušahu gdje govorahu jezike, i velièahu Boga. Tada odgovori Petar:
47 “Wani zai iya hana a yi wa waɗannan mutane baftisma da ruwa? Sun karɓi Ruhu Mai Tsarki kamar yadda muka karɓa.”
Eda može ko vodu zabraniti da se ne krste oni koji primiše Duha svetoga kao i mi?
48 Saboda haka ya ba da umarni a yi musu baftisma cikin sunan Yesu Kiristi. Sa’an nan suka roƙi Bitrus yă zauna da su na’yan kwanaki.
I zapovjedi im da se krste u ime Isusa Hrista. Tada ga moliše da ostane kod njih nekoliko dana.