< Ayyukan Manzanni 10 >

1 A Kaisariya akwai wani mutum mai suna Korneliyus, wani jarumin Roma ne, a ƙungiyar soja da ake kira Bataliyar Italiya.
Now there was a certain man in Cesarea, named Cornelius, a centurion that called the Italian Band,
2 Shi da dukan iyalinsa masu ibada ne masu tsoron Allah kuma; yakan ba da kyauta hannu sake ga masu bukata yana kuma addu’a ga Allah ba fasawa.
a man of piety, and one that feared God, with all his house; giving, also, much alms to the people, and praying to God continually.
3 Wata rana wajen ƙarfe uku na yamma ya ga wahayi. A sarari ya ga wani mala’ikan Allah, wanda ya zo wajensa ya ce, “Korneliyus!”
He evidently saw, in a vision, about the ninth hour of the day, a messenger of God coming in to him, and saying to him, Cornelius!
4 Korneliyus kuwa ya zura masa ido a tsorace ya ce, “Mene ne, ya Ubangiji?” Mala’ikan ya ce, “Addu’o’inka da kyautanka ga matalauta sun kai har sama, hadayar tunawa ce a gaban Allah.
And having fixed his eyes upon him, he was afraid, and said, What is it, Lord? And he said to him, Your prayers and your alms are come up, as a memorial before God.
5 Yanzu sai ka aiki mutane zuwa Yoffa su dawo da wani mutum mai suna Siman wanda ake kira Bitrus.
And now send men to Joppa and bring hither Simon, whose surname is Peter:
6 Yana zama tare da Siman, mai aikin fatu, wanda gidansa ke bakin teku.”
he lodges with one Simon, a tanner, whose house is by the seaside.
7 Sa’ad da mala’ikan da ya yi masa magana ya tafi, sai Korneliyus ya kira biyu daga cikin bayinsa da kuma wani soja mai ibada wanda yake ɗaya a cikin masu yin masa hidima.
As soon as the messenger, who spoke to Cornelius, was gone, he called two of his domestics, and a pious soldier, of them that waited upon him;
8 Ya fada musu duk abin da ya faru sa’an nan ya aike su Yoffa.
and having related to them all these things, he sent them to Joppa.
9 Wajen tsakar rana kashegari yayinda suke cikin tafiyarsu suna kuma dab da birnin, sai Bitrus ya hau bisan rufin gida yă yi addu’a.
On the next day, while they were on their journey, and drew near the city, Peter went up to the top of the house to pray, about the sixth hour.
10 Yunwa ta kama shi ya kuwa so yă ci wani abu, yayinda ake shirya abinci, sai wahayi ya zo masa.
And he was hungry, and would have taken a little refreshment; but while they were preparing, he fell into an ecstasy;
11 Ya ga sama ya buɗe ana kuwa saukowa wani abu ƙasa kamar babban mayafi zuwa duniya ta kusurwansa huɗu.
and he saw heaven opened, and something descending like a great sheet, fastened at the four corners, and let down to the earth:
12 Cikinsa kuwa akwai kowace irin dabba mai ƙafa huɗu da masu ja da ciki na duniya da kuma tsuntsayen sararin sama.
in which there were all sorts of things, even four-footed animals of the earth, and wild beasts, and reptiles, and fowls of the air.
13 Sa’an nan wata murya ta ce masa, “Bitrus, ka tashi. Ka yanka ka ci.”
And there came a voice to him, Rise, Peter, kill, and eat.
14 Bitrus ya ce, “Sam, Ubangiji! Ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko marar tsabta ba.”
But Peter said, By no means, Lord; for I have never eat anything which is common or unclean.
15 Muryar ta yi magana da shi sau na biyu ta ce, “Kada ka ce da abin da Allah ya tsarkake marar tsarki.”
And the voice said to him again, the second time, Those things which God has cleansed, do not you call common.
16 Wannan ya faru har sau uku, sai nan da nan aka ɗauke mayafin zuwa sama.
And this was done three times, and the sheet was taken up again into heaven.
17 Tun Bitrus yana cikin tunani game da ma’anar wahayin nan, sai ga mutanen da Korneliyus ya aika sun sami gidan Siman suna kuma tsaye a ƙofar.
While Peter was pondering in himself, what the vision, which he had seen, might import; behold, the men, who were sent from Cornelius, having inquired out the house of Simon, stood at the door;
18 Suka yi sallama, suna tambaya ko Siman wanda aka sani da suna Bitrus yana zama a can.
and calling, they asked, if Simon, whose surname was Peter, lodged there.
19 Yayinda Bitrus yana cikin tunani game da wahayin, sai Ruhu ya ce masa, “Siman, ga mutum uku suna nemanka.
Now, as Peter was reflecting on this vision; the Spirit said to him, Behold, three men are inquiring for you:
20 Saboda haka ka tashi ka sauka. Kada ka yi wata-wata, gama ni ne na aiko su.”
arise, therefore, go down, and go with them without hesitation; for I have sent them.
21 Sai Bitrus ya sauka ya ce wa mutanen, “Ni ne kuke nema. Me ya kawo ku?”
Then Peter went down to the men, who were sent to him from Cornelius, and said, Behold, I am the man whom you seek; what is the cause of your coming?
22 Mutanen suka amsa, “Mun zo ne daga wurin Korneliyus wani jarumin. Shi mutum ne mai adalci mai tsoron Allah kuma, wanda dukan Yahudawa ke girmamawa. Wani mala’ika mai tsarki ya faɗa masa, yă sa ka zo gidansa don yă ji abin da za ka faɗa.”
And they said, Cornelius, the centurion, a righteous man, who fears God, and has a character attested by all the Jewish people, has been instructed, by a holy messenger, to send for you to his house, and to hear words from you.
23 Sai Bitrus ya gayyaci mutanen cikin gida su zama baƙinsa. Kashegari Bitrus ya tafi tare da su, waɗansu’yan’uwa daga Yoffa kuwa suka tafi tare da shi.
Having, therefore, called them in, he entertained them, and the next day set out with them: and some of the brethren, who were of Joppa, went with him.
24 Kashegari sai ya iso Kaisariya. Korneliyus kuwa yana nan yana jiransu, ya kuma gayyaci’yan’uwansa da abokansa na kusa.
And the next day they entered into Cesarea; and Cornelius was waiting for them, having called together his relations and intimate friends.
25 Da Bitrus ya shiga gidan, Korneliyus ya sadu da shi ya kuma fāɗi a gabansa cikin bangirma.
Now, as Peter was coming in, Cornelius met him, and prostrating himself at his feet, made obeisance.
26 Amma Bitrus ya sa shi ya tashi. Ya ce, “Tashi, ni mutum ne kawai.”
But Peter raised him up, saying, Arise; I also am a man.
27 Yana magana da shi, sai Bitrus ya shiga ciki ya kuma tarar da taron mutane da yawa.
And discoursing with him, he went in, and found many gathered together.
28 Sai ya ce musu, “Ku da kanku kun san cewa dokarmu ta hana mutumin Yahuda yin cuɗanya, ko ya ziyarci Ba’al’umme. Amma Allah ya nuna mini cewa kada in kira wani mutum marar tsarki ko marar tsabta.
And he said to them, You know that it is unlawful for a man that is a Jew to join with, or to come into the house of, one of another nation; nevertheless, God has shown me that I am to call no man common or unclean.
29 Don haka sa’ad da aka aika in zo, na zo ba wata faɗa. To, ko zan san abin da ya sa ka aika in zo?”
Wherefore, when I was sent for, I came without debate: I ask, therefore, on what account you have sent for me?
30 Korneliyus ya amsa ya ce, “Kwana huɗu da suka wuce ina a gidana ina addu’a a wannan lokaci, wajen ƙarfe uku na yamma. Ba zato ba tsammani sai ga wani mutum cikin tufafi masu walƙiya ya tsaya a gabana
And Cornelius said, Four days ago, I was fasting till this hour; and at the ninth hour I prayed in my house; and, behold, a man stood before me in bright raiment,
31 ya ce, ‘Korneliyus, Allah ya ji addu’arka, ya kuma tuna da kyautanka ga matalauta.
and said, Cornelius, your prayer is heard, and your alms are remembered before God:
32 Ka aika zuwa Yoffa don a kira Siman wanda ake ce da shi Bitrus. Shi baƙo ne a gidan Siman mai aikin fatu, wanda yake zama a bakin teku.’
send, therefore, to Joppa, and call hither Simon, whose surname is Peter; he lodges in the house of one Simon, a tanner, by the seaside; who, when he is come, shall speak to you.
33 Saboda haka na aika a zo da kai nan da nan, ya kuma yi kyau da ka zo. To ga mu duka a nan a gaban Allah don mu saurari dukan abin da Ubangiji ya umarce ka ka faɗa mana.”
Immediately, therefore, I sent to you, and you have done well in coming. Now, therefore, we are all here present before God, to hear all things which God has given to you in charge.
34 Sa’an nan Bitrus ya fara magana ya ce, “Yanzu na gane yadda gaskiya ne cewa Allah ba ya sonkai
Then Peter, opening his mouth, said, Of a truth, I perceive that God is no respecter of persons;
35 amma yana karɓan mutane daga kowace al’ummar da take tsoronsa suke kuma aikata abin da yake daidai.
but, in every nation, he that fears him, and works of righteousness, is acceptable to him.
36 Kun san saƙon da Allah ya aika wa mutanen Isra’ila, yana shelar labari mai daɗi na salama ta wurin Yesu Kiristi, shi ne kuwa Ubangijin kowa.
This is that message which he sent to the children of Israel; proclaiming the glad tidings of peace by Jesus Christ, who is Lord of all.
37 Kun san abin da ya faru a dukan Yahudiya, farawa daga Galili bayan baftismar da Yohanna ya yi wa’azi,
You know the report there was, through all Judea, which began from Galilee, after the immersion which John preached,
38 yadda Allah ya shafe Yesu Banazare da Ruhu Mai Tsarki da kuma iko, da kuma yadda ya zaga ko’ina yana aikata alheri yana kuma warkar da dukan waɗanda suke ƙarƙashin ikon Iblis, domin Allah yana tare da shi.
concerning Jesus of Nazareth; how God anointed him with the Holy Spirit, and with power; who went about doing good, and healing all who were oppressed by the devil; for God was with him.
39 “Mu kuwa shaidu ne na dukan abin da ya yi a ƙasar Yahudawa da kuma a Urushalima. Suka kashe shi ta wurin rataye shi a kan itace,
And we are witnesses of all things which he did, both in the region of the Jews, and in Jerusalem: whom they slew, hanging him on a tree.
40 amma Allah ya tashe shi daga matattu a rana ta uku, ya sa kuma aka gan shi.
This very person God raised up, on the third day, and granted him to become manifest;
41 Ba dukan mutane ne suka gan shi ba, amma ta wurin shaidun da Allah ya riga ya zaɓa, ta wurinmu da muka ci muka kuma sha tare da shi bayan tashinsa daga matattu.
not to all the people, but to witnesses before appointed by God, even to us, who have eat and drunk with him after he arose from the dead.
42 Ya umarce mu mu yi wa’azi ga mutane mu kuma shaida cewa shi ne wanda Allah ya naɗa yă zama mai shari’a na masu rai da na matattu.
And he has given in charge to us to proclaim to the people, and to testify that it is he who is appointed by God, to be the judge of the living and the dead.
43 Duk annabawa sun yi shaida game da shi cewa duk wanda ya ba da gaskiya gare shi zai sami gafarar zunubai ta wurin sunansa.”
To him all the prophets bear witness, that every one who believes on him, shall receive forgiveness of sins by his name.
44 Tun Bitrus yana cikin faɗin waɗannan kalmomi, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauka wa duk waɗanda suka ji saƙon.
While Peter was yet speaking these words, the Holy Spirit fell upon all who were hearing the word:
45 Masu bin da suke da kaciya waɗanda suka zo tare da Bitrus suka yi mamaki cewa an ba da kyautar Ruhu Mai Tsarki har ma a kan Al’ummai.
and they of the circumcision, who believed, as many as came with Peter, were astonished that the gift of the Spirit was poured out upon the Gentiles also:
46 Gama sun ji su suna magana da waɗansu harsuna suna kuma yabon Allah. Sai Bitrus ya ce,
for they heard them speaking in diverse languages, and glorifying God.
47 “Wani zai iya hana a yi wa waɗannan mutane baftisma da ruwa? Sun karɓi Ruhu Mai Tsarki kamar yadda muka karɓa.”
Then Peter answered, Can any one forbid water, that these persons should not be immersed, who have received the Holy Spirit as well as we?
48 Saboda haka ya ba da umarni a yi musu baftisma cikin sunan Yesu Kiristi. Sa’an nan suka roƙi Bitrus yă zauna da su na’yan kwanaki.
And he ordered them to be immersed in the name of the Lord. And they entreated him to continue with them several days.

< Ayyukan Manzanni 10 >