< Ayyukan Manzanni 1 >

1 A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
Ukulandisa kokuqala ngakwenza, Teyofilu, ngakho konke uJesu aqala kokubili ukukwenza lokukufundisa,
2 har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
kwaze kwaba lusuku akhutshulwa ngalo, esebalayile ngoMoya oNgcwele abaphostoli ayebakhethile;
3 Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
wazibonakalisa futhi kubo ephilile emva kokuhlupheka kwakhe ngobufakazi obunengi obuqinisekileyo, wabonwa yibo okwensuku ezingamatshumi amane, ekhuluma ngezinto ezimayelana lombuso kaNkulunkulu.
4 A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
Kwathi ehlangene labo, wabalaya ukuthi bangasuki eJerusalema, kodwa balindele isithembiso sikaBaba, elasizwa ngami;
5 Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
ngoba ngeqiniso uJohane wabhabhathiza ngamanzi, kodwa lina lizabhabhathizwa ngoMoya oNgcwele kungakadluli insuku ezinengi.
6 Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
Kwathi sebebuthene bambuza bathi: Nkosi, uzabuyisela umbuso kuIsrayeli kulesisikhathi yini?
7 Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
Wasesithi kubo: Kakusikho okwenu ukwazi izikhathi kumbe imizuzu ayimisileyo uBaba ngawakhe amandla;
8 Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
kodwa lizakwemukela amandla, esefikile phezu kwenu uMoya oNgcwele; njalo libe ngabafakazi bami eJerusalema kanye layo yonke iJudiya leSamariya, njalo kuze kube semkhawulweni womhlaba.
9 Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
Kwathi esetshilo lezizinto, wakhutshulwa bekhangele, leyezi lamsusa emehlweni abo.
10 Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
Bathi besajolozele ezulwini, esenyuka, njalo khangela, amadoda amabili ema labo elezembatho ezimhlophe,
11 Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
njalo athi: Madoda maGalili, limeleni lijolozele ezulwini? UJesu lo, osuswe kini wenyukiselwa ezulwini, uzabuya ngokunjalo ngendlela elimbone esiya ngayo ezulwini.
12 Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
Basebebuyela eJerusalema bevela entabeni ethiwa ngeyoMhlwathi, eseduze leJerusalema, ummango wohambo lwesabatha.
13 Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
Kwathi sebengenile, benyukela endlini ephezulu, lapho ababehlala khona, uPetro loJakobe loJohane loAndreya, uFiliphu loTomasi, uBartolomewu loMathewu, uJakobe kaAlfewu loSimoni umZelothi, loJudasi kaJakobe.
14 Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
Bonke laba baphikelela bengqondonye emkhulekweni lekuncengeni, kanye labesifazana loMariya unina kaJesu, njalo labafowabo.
15 A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
Kwathi ngalezonsuku uPetro wasukuma phakathi kwabafundi, kwakulexuku labantu ndawonye elalingaba likhulu lamatshumi amabili, wathi:
16 ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
Madoda bazalwane, kwakumele ukuthi lumbhalo ugcwaliswe, uMoya oyiNgcwele awukhuluma ngaphambili ngomlomo kaDavida ngoJudasi, owayengumkhokheli walabo abambambayo uJesu,
17 dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
ngoba wayebalwe kanye lathi, njalo wemukela isabelo salinkonzo.
18 (Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
Lo-ke wathenga isiqinti ngomvuzo wobubi, wawa ngekhanda waqhekezeka phakathi, lemibilini yakhe yonke yachitheka.
19 Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
Njalo kwaziwa yibo bonke abakhileyo eJerusalema, saze sabizwa lesosiqinti ngolimi lwakibo ngokuthi iAkeldama, okuyikuthi iSiqinti segazi.
20 Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
Ngoba kulotshiwe egwalweni lweziHlabelelo ukuthi: Umuzi wakhe kawube lunxiwa, njalo kungabi khona ohlala kuwo; lokuthi: Omunye kathathe ubuphathi bakhe.
21 Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
Ngakho kumele ukuthi kulawomadoda ayehamba lathi kuso sonke isikhathi lapho iNkosi uJesu yayingena njalo iphuma phakathi kwethu,
22 farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
kusukela ebhabhathizweni lukaJohane, kwaze kwaba lusuku akhutshulwa ngalo kithi, omunye wabo kabe ngumfakazi kanye lathi wokuvuka kwakhe.
23 Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
Basebemisa ababili, uJosefa othiwa nguBarsaba, othiwa futhi nguJustusi, loMathiyasi.
24 Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
Basebekhuleka besithi: Wena Nkosi, wena owaziyo inhliziyo zabo bonke, tshengisa kulaba ababili oyedwa, omkhethileyo,
25 ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
ukwemukela isabelo kulinkonzo lobuphostoli, uJudasi aphambuka kuso, ukuthi aye endaweni engeyakhe.
26 Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.
Basebebapha inkatho yabo; lenkatho yadla uMathiyasi, wasebalwa kanye labaphostoli abalitshumi lanye.

< Ayyukan Manzanni 1 >