< Ayyukan Manzanni 1 >

1 A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
The former account, indeed, I made concerning all things, O Theophilus, that Jesus began both to do and to teach,
2 har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
until the day in which, having given command through the Holy Spirit to the apostles whom He chose out, He was taken up,
3 Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
to whom He also presented Himself alive after His suffering, in many certain proofs, being seen by them through forty days, and speaking the things concerning the Kingdom of God.
4 A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
And being assembled together with them, He commanded them not to depart from Jerusalem, but to wait for the promise of the Father, “Which you heard from Me;
5 Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
because John, indeed, immersed in water, but you will be immersed in the Holy Spirit not many days after these.”
6 Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
They, therefore, indeed, having come together, were questioning Him, saying, “Lord, do You at this time restore the kingdom to Israel?”
7 Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
And He said to them, “It is not yours to know times or seasons that the Father appointed in His own authority;
8 Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
but you will receive power at the coming of the Holy Spirit on you, and you will be witnesses for Me both in Jerusalem, and in all Judea and Samaria, and to the end of the earth.”
9 Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
And having said these things—they beholding—He was taken up, and a cloud received Him up from their sight;
10 Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
and as they were looking steadfastly to the sky in His going on, then, behold, two men stood by them in white clothing,
11 Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
who also said, “Men, Galileans, why do you stand gazing into the sky? This Jesus who was received up from you into Heaven, will so come in what manner you saw Him going on to Heaven.”
12 Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
Then they returned to Jerusalem from [that] called the Mount of Olives, that is near Jerusalem, a Sabbath’s journey;
13 Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
and when they came in, they went up into the upper room, where were abiding both Peter, and James, and John, and Andrew, Philip, and Thomas, Bartholomew, and Matthew, James, of Alphaeus, and Simon the Zealot, and Judas, of James;
14 Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
these were all continuing with one accord in prayer and supplication, with women, and Mary the mother of Jesus, and with His brothers.
15 A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
And in these days, Peter having risen up in the midst of the disciples, said (also the multitude of the names at the same place was, as it were, one hundred and twenty),
16 ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
“Men, brothers, it was necessary [for] this Writing to be fulfilled that the Holy Spirit spoke beforehand through the mouth of David, concerning Judas, who became guide to those who took Jesus,
17 dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
because he was numbered among us, and received the share in this ministry.
18 (Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
(This one, indeed, then, purchased a field out of the reward of unrighteousness, and falling headlong, burst apart in the midst, and all his bowels gushed forth,
19 Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
and it became known to all those dwelling in Jerusalem, insomuch that this place is called, in their proper dialect, Aceldama, that is, Field of Blood.)
20 Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
For it has been written in [the] Scroll of Psalms: Let his lodging-place become desolate, and let no one be dwelling in it, and let another take his oversight.
21 Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
It is necessary, therefore, of the men who went with us during all the time in which the Lord Jesus went in and went out among us,
22 farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
beginning from the immersion of John, to the day in which He was received up from us, one of these to become with us a witness of His resurrection.”
23 Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
And they set two, Joseph called Barsabas, who was surnamed Justus, and Matthias,
24 Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
and having prayed, they said, “You, LORD, who are knowing the heart of all, show which one You chose of these two,
25 ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
to receive the share of this ministry and apostleship, from which Judas, by transgression, fell, to go on to his proper place”;
26 Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.
and they gave their lots, and the lot fell on Matthias, and he was numbered with the eleven apostles.

< Ayyukan Manzanni 1 >