< Ayyukan Manzanni 1 >

1 A littafina na farko, Tiyofilus, na rubuta game da dukan abin da Yesu ya fara yi, da abin da ya koyar
Prvu sam knjigu, Teofile, sastavio o svemu što je Isus činio i učio
2 har zuwa ranar da aka ɗauke shi zuwa sama, bayan ya ba da umarnai ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa.
do dana kad je uznesen pošto je dao upute apostolima koje je izabrao po Duhu Svetome.
3 Bayan wahalarsa, ya bayyana kansa ga waɗannan mutane ya kuma ba da tabbatattun alamu masu yawa cewa yana da rai. Ya bayyana a gare su har kwana arba’in ya kuma yi musu magana game da mulkin Allah.
Njima je poslije svoje muke mnogim dokazima pokazao da je živ, četrdeset im se dana ukazivao i govorio o kraljevstvu Božjem.
4 A wani lokaci, yayinda yake ci tare da su, ya ba su wannan umarni, “Kada ku bar Urushalima, amma ku jira kyautar da Ubana ya yi alkawari, wadda kuka ji na yi magana a kai.
I dok je jednom s njima blagovao, zapovjedi im da ne napuštaju Jeruzalema, nego neka čekaju Obećanje Očevo “koje čuste od mene:
5 Gama Yohanna ya yi baftisma daruwa, amma a cikin’yan kwanaki za a yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki.”
Ivan je krstio vodom, a vi ćete naskoro nakon ovih dana biti kršteni Duhom Svetim.”
6 Saboda haka, sa’ad da suka taru, sai suka tambaye shi, “Ubangiji, a wannan lokaci za ka mayar da mulki ga Isra’ila?”
Nato ga sabrani upitaše: “Gospodine, hoćeš li u ovo vrijeme Izraelu opet uspostaviti kraljevstvo?”
7 Ya ce musu, “Ba naku ba ne ku san lokuta ko ranakun da Uban ya shirya cikin ikonsa.
On im odgovori: “Nije vaše znati vremena i zgode koje je Otac podredio svojoj vlasti.
8 Amma ku za ku karɓi iko sa’ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauka a kanku; za ku kuma zama shaiduna cikin Urushalima, da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, zuwa kuma iyakar duniya.”
Nego primit ćete snagu Duha Svetoga koji će sići na vas i bit ćete mi svjedoci u Jeruzalemu, po svoj Judeji i Samariji i sve do kraja zemlje.”
9 Bayan ya faɗi wannan, sai aka ɗauke shi sama a idanunsu sai wani girgije ya rufe shi daga ganinsu.
Kada to reče, bi uzdignut njima naočigled i oblak ga ote njihovim očima.
10 Suna zuba ido a bisa, zuwa cikin sararin sama yayinda yake tafiya, nan da nan, sai ga mutane biyu saye da fararen riguna tsaye kusa da su.
I dok su netremice gledali kako on odlazi na nebo, gle, dva čovjeka stadoše kraj njih u bijeloj odjeći
11 Sai suka ce, “Mutanen Galili, don me kuke tsaye a nan kuna duban sararin sama? Wannan Yesu, wanda aka ɗauke daga gare ku zuwa sama, zai komo daidai yadda kuka ga ya tafi sama.”
i rekoše im: “Galilejci, što stojite i gledate u nebo? Ovaj Isus koji je od vas uznesen na nebo isto će tako doći kao što ste vidjeli da odlazi na nebo.”
12 Sai suka koma Urushalima daga tudun da ake kira Dutsen Zaitun, tafiyar ranar Asabbaci guda daga birnin.
Onda se vratiše u Jeruzalem s brda zvanoga Maslinsko, koje je blizu Jeruzalema, udaljeno jedan subotni hod.
13 Da suka iso, sai suka hau gidan sama, zuwa ɗakin da suke zama. Waɗanda suka kasance kuwa su ne, Bitrus, Yohanna, Yaƙub da Andarawus; Filibus da Toma; Bartolomeyu da Mattiyu; Yaƙub ɗan Alfayus da Siman Zilot, da kuma Yahuda ɗan Yaƙub.
I pošto uđu u grad, uspnu se u gornju sobu gdje su boravili: Petar i Ivan i Jakov i Andrija, Filip i Toma, Bartolomej i Matej, Jakov Alfejev i Šimun Revnitelj i Juda Jakovljev -
14 Waɗannan duka suka duƙufa cikin addu’a, tare da waɗansu mata da Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma tare da’yan’uwansa.
svi oni bijahu jednodušno postojani u molitvi sa ženama, i Marijom, majkom Isusovom, i braćom njegovom.
15 A waɗancan kwanakin Bitrus ya miƙe tsaye cikin’yan’uwa masu bi (taron da ya yi kusan mutum ɗari da ashirin)
U one dane ustade Petar među braćom - a bijaše sakupljenog naroda oko sto i dvadeset duša - i reče:
16 ya ce, “’Yan’uwana, dole a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya yi magana tun da daɗewa ta bakin Dawuda game da Yahuda, wanda ya zama jagora ga waɗanda suka kama Yesu
“Braćo! Trebalo je da se ispuni Pismo što ga na usta Davidova proreče Duh Sveti o Judi koji bijaše vođa onih što uhvatiše Isusa.
17 dā shi ɗaya ne cikinmu, ya kuma yi hidima a cikin aikin nan.”
A Juda se ubrajao među nas i imao udio u ovoj službi.
18 (Da ladar da ya samu saboda muguntarsa Yahuda ya sayi wani fili; a can ya fāɗi da kā, jikinsa ya fashe, hanjinsa kuma duk suka zubo.
On, eto, steče predio cijenom nepravednosti pa se stropošta, raspuče po sredini i razli mu se sva utroba.
19 Kowa a Urushalima ya ji game da wannan, saboda haka suka kira wannan filin Akeldama, da yarensu, wato, Filin Jini.)
I svim je Jeruzalemcima znano da se onaj predio njihovim jezikom zove Akeldama, to jest Predio smrti.
20 Bitrus ya ce, “Gama yana a rubuce a cikin Littafin Zabura cewa, “‘Bari wurinsa yă zama babu kowa; kada kowa ya zauna a cikinsa,’ kuma, “‘Bari wani ya ɗauki matsayinsa na shugabanci.’
Pisano je doista u Knjizi psalama: Njegova kuća nek opusti, nek ne bude stanovnika u njoj! Njegovo nadgledništvo nek dobije drugi!
21 Saboda haka dole a zaɓi ɗaya daga cikin mutanen da suke tare da mu duk lokacin da Ubangiji Yesu yake shiga da fita a cikinmu,
Jedan dakle od ovih ljudi što bijahu s nama za sve vrijeme što je među nama živio Gospodin Isus -
22 farawa daga baftisma ta Yohanna har zuwa sa’ad da aka ɗauke Yesu daga gare mu. Gama dole ɗaya daga waɗannan ya zama shaidar tashinsa daga matattu tare da mu.”
počevši od krštenja Ivanova pa sve do dana kad bi uzet od nas - treba da bude svjedokom njegova uskrsnuća.
23 Saboda haka suka gabatar da mutane biyu. Yusuf mai suna Barsabbas (da aka kuma sani da Yustus) da kuma Mattiyas.
I postaviše dvojicu: Josipa koji se zvao Barsaba a prozvao se Just, i Matiju.
24 Sai suka yi addu’a suka ce, “Ubangiji, ka san zuciyar kowa. Nuna mana wanne a cikin waɗannan biyu da ka zaɓa
Onda se pomoliše: “Ti, Gospodine, poznavaoče svih srdaca, pokaži koga si od ove dvojice izabrao
25 ya karɓi wannan aikin manzanci, wanda Yahuda ya bari don yă tafi wurin da yake nasa.”
da primi mjesto ove apostolske službe kojoj se iznevjeri Juda da ode na svoje mjesto.”
26 Sa’an nan suka jefa ƙuri’u, ƙuri’ar kuwa ta fāɗo a kan Mattiyas; sai aka sa shi cikin manzannin nan goma sha ɗaya.
Onda baciše kocke i kocka pade na Matiju; tako bi pribrojen jedanaestorici apostola.

< Ayyukan Manzanni 1 >