< 3 Yohanna 1 >

1 Dattijon nan, Zuwa ga ƙaunataccen abokina Gayus, wanda nake ƙauna ƙwarai da gaske.
prācīno 'haṁ satyamatād yasmin prīye taṁ priyatamaṁ gāyaṁ prati patraṁ likhāmi|
2 Abokina ƙaunatacce, ina addu’a ka sami zaman lafiya don kome yă yi maka daidai, kamar yadda ruhunka yake zaune lafiya.
he priya, tavātmā yādṛk śubhānvitastādṛk sarvvaviṣaye tava śubhaṁ svāsthyañca bhūyāt|
3 Na yi farin ciki ƙwarai sa’ad da waɗansu’yan’uwa suka zo suka yi zance game da yadda kake da aminci ga gaskiyan nan da kuma yadda kake cin gaba cikin gaskiyan nan.
bhrātṛbhirāgatya tava satyamatasyārthatastvaṁ kīdṛk satyamatamācarasyetasya sākṣye datte mama mahānando jātaḥ|
4 Ba abin da ya fi sa ni farin ciki fiye da in ji cewa’ya’yana suna cikin gaskiyan nan.
mama santānāḥ satyamatamācarantītivārttāto mama ya ānando jāyate tato mahattaro nāsti|
5 Abokina ƙaunatacce, kana da aminci cikin abin da kake yi wa’yan’uwa, ko da yake su baƙi ne a gare ka.
he priya, bhrātṛn prati viśeṣatastān videśino bhṛtṛn prati tvayā yadyat kṛtaṁ tat sarvvaṁ viśvāsino yogyaṁ|
6 Sun faɗa wa ikkilisiya game da ƙaunarka. Za ka kyauta in ka sallame su a hanyar da ta cancanci Allah.
te ca samiteḥ sākṣāt tava pramnaḥ pramāṇaṁ dattavantaḥ, aparam īśvarayogyarūpeṇa tān prasthāpayatā tvayā satkarmma kāriṣyate|
7 Saboda Sunan nan ne suka fito, ba sa karɓan wani taimako daga waɗanda ba masu bi ba.
yataste tasya nāmnā yātrāṁ vidhāya bhinnajātīyebhyaḥ kimapi na gṛhītavantaḥ|
8 Saboda haka ya kamata mu nuna halin karɓan baƙi ga irin mutanen nan domin mu yi aiki tare saboda gaskiyan nan.
tasmād vayaṁ yat satyamatasya sahāyā bhavema tadarthametādṛśā lokā asmābhiranugrahītavyāḥ|
9 Na rubuta wa ikkilisiya, amma Diyotirefes, wanda yake son zama na farko, ya ƙi yă yi hulɗa da mu.
samitiṁ pratyahaṁ patraṁ likhitavān kintu teṣāṁ madhye yo diyatriphiḥ pradhānāyate so 'smān na gṛhlāti|
10 Saboda haka in na zo, zan tone abin da yake yi, yana surutu game da mu, yana ɓaɓɓata mu. Wannan ma bai ishe shi ba, har yana ƙin marabtar’yan’uwa. Yana hana waɗanda suke so yin haka, yana ma korinsu daga ikkilisiya.
ato 'haṁ yadopasthāsyāmi tadā tena yadyat kriyate tat sarvvaṁ taṁ smārayiṣyāmi, yataḥ sa durvvākyairasmān apavadati, tenāpi tṛptiṁ na gatvā svayamapi bhrātṛn nānugṛhlāti ye cānugrahītumicchanti tān samitito 'pi bahiṣkaroti|
11 Abokina ƙaunatacce, kada ka yi koyi da abin da yake mugu sai dai abin da yake nagari. Duk mai yin abin da yake nagari daga Allah yake. Duk mai yin abin da yake mugu bai taɓa sanin Allah ba.
he priya, tvayā duṣkarmma nānukriyatāṁ kintu satkarmmaiva| yaḥ satkarmmācārī sa īśvarāt jātaḥ, yo duṣkarmmācārī sa īśvaraṁ na dṛṣṭavān|
12 Demetiriyus yana da shaida mai kyau daga wurin kowa, har gaskiya kanta ma ta shaide shi. Mu ma muna ba da shaida mai kyau a kansa, ka kuma san cewa shaidarmu gaskiya ce.
dīmītriyasya pakṣe sarvvaiḥ sākṣyam adāyi viśeṣataḥ satyamatenāpi, vayamapi tatpakṣe sākṣyaṁ dadmaḥ, asmākañca sākṣyaṁ satyameveti yūyaṁ jānītha|
13 Ina da abubuwa da dama da zan rubuta maka, sai dai ba na so in yi amfani da alƙalami da inki in rubuta su.
tvāṁ prati mayā bahūni lekhitavyāni kintu masīlekhanībhyāṁ lekhituṁ necchāmi|
14 Ina fata in gan ka nan ba da daɗewa ba, za mu kuwa yi magana fuska da fuska. Salama gare ka. Abokai a nan suna gaishe ka. Ka gai da abokai a can da sunansu.
acireṇa tvāṁ drakṣyāmīti mama pratyāśāste tadāvāṁ sammukhībhūya parasparaṁ sambhāṣiṣyāvahe| tava śānti rbhūyāt| asmākaṁ mitrāṇi tvāṁ namaskāraṁ jñāpayanti tvamapyekaikasya nāma procya mitrebhyo namaskuru| iti|

< 3 Yohanna 1 >