< 2 Timoti 1 >

1 Bulus, manzon Kiristi Yesu ta wurin nufin Allah, bisa ga alkawarin rai wanda yake cikin Kiristi Yesu,
Paul, an Apostle of Christ Jesus, by the will of God, for proclaiming the promise of the Life which is in Christ Jesus:
2 Zuwa ga Timoti, ƙaunataccen ɗana. Alheri, jinƙai da salama daga Allah Uba da kuma Kiristi Yesu Ubangijinmu, su kasance tare da kai.
To Timothy my dearly-loved child. May grace, mercy and peace be granted to you from God the Father and Christ Jesus our Lord.
3 Na gode wa Allah wanda nake bauta wa, kamar yadda kakanni-kakannina suka yi da lamiri mai tsabta, yadda kullum dare da rana ina tuna da ku a cikin addu’o’ina.
I thank God, whom I serve with a pure conscience--as my forefathers did--that night and day I unceasingly remember you in my prayers,
4 Sa’ad da na tuna da hawayenka, nakan yi marmarin ganinka, don in cika da farin ciki.
being always mindful of your tears, and longing to see you that I may be filled with joy.
5 An tunashe ni da sahihiyar bangaskiyarka, wadda a farko ta kasance a cikin kakarka Loyis da kuma mahaifiyarka Yunis yanzu kuwa na tabbata tana cikinka.
For I recall the sincere faith which is in your heart--a faith which dwelt first in your grandmother Lois and then in your mother Eunice, and, I am fully convinced, now dwells in you also.
6 Saboda haka, ina so in faɗakar da kai, ka lura baiwan nan ta Allah, wadda take tare da kai ta wurin ɗibiya maka hannuwana.
For this reason let me remind you to rekindle God's gift which is yours through the laying on of my hands.
7 Gama Allah bai ba mu ruhun tsoro ba, sai dai ruhun iko, na ƙauna da kuma na kamunkai.
For the Spirit which God has given us is not a spirit of cowardice, but one of power and of love and of sound judgement.
8 Saboda haka kada ka ji kunyar ba da shaida game da Ubangijinmu, ko kuwa ka ji kunyata, ni da nake ɗan sarƙa saboda shi. Sai dai ka haɗa kai tare da ni cikin shan wahala saboda bishara ta wurin ikon Allah,
Do not be ashamed then to bear witness for our Lord and for me His prisoner; but rather share suffering with me in the service of the Good News, strengthened by the power of God.
9 wanda ya cece mu ya kuma kira mu ga rayuwar tsarki ba saboda wani abin da muka yi ba sai dai saboda nufinsa da kuma alherinsa. An ba mu wannan alheri cikin Kiristi Yesu tun fil azal, (aiōnios g166)
For He saved us and called us with a holy call, not in accordance with our desserts, but in accordance with His own purpose and the free grace which He bestowed on us in Christ Jesus before the commencement of the Ages, (aiōnios g166)
10 amma yanzu an bayyana ta ta wurin bayyanuwar Mai Cetonmu, Kiristi Yesu, wanda ya hallaka mutuwa ya kuma kawo rai da rashin mutuwa a sarari ta wurin bishara.
but which has now been plainly revealed through the Appearing of our Saviour, Christ Jesus. He has put an end to death and has brought Life and Immortality to light through the Good News,
11 A wannan bishara ce, aka naɗa ni mai shela da manzo da kuma malami.
of which I have been appointed a preacher, Apostle and teacher, to the Gentiles.
12 Shi ya sa nake shan wahalar da nake sha. Duk da haka ba na jin kunya, domin na san wanda na gaskata da shi, na kuma tabbata cewa yana iya kiyaye abin da na danƙa masa amana don wancan rana.
That indeed is the reason why I suffer as I do. But I am not ashamed, for I know in whom my trust reposes, and I am confident that He has it in His power to keep what I have entrusted to Him safe until that day.
13 Abin da ka ji daga gare ni, ka kiyaye shi kamar tsarin sahihiyar koyarwa, cikin bangaskiya da ƙauna cikin Kiristi Yesu.
Provide yourself with an outline of the sound teaching which you have heard from my lips, and be true to the faith and love which are in Christ Jesus.
14 Ka kiyaye kyakkyawar ajiyan nan da aka danƙa maka amana, ka lura da ita da taimakon Ruhu Mai Tsarki wanda yake raye a cikinmu.
That precious treasure which is in your charge, guard through the Holy Spirit who has His home in our hearts.
15 Ka san cewa kowa a lardin Asiya ya juya mini baya, har da Figelus da Hermogenes.
Of this you are aware, that all the Christians in Roman Asia have deserted me: and among them Phygelus and Hermogenes.
16 Bari Ubangiji yă yi wa iyalin Onesiforus jinƙai, domin sau da dama yakan wartsakar da ni, bai kuma ji kunyar sarƙoƙina ba.
May the Lord show mercy to the household of Onesiphorus; for many a time he cheered me and he was not ashamed of my chain.
17 A maimakon haka ma, sa’ad da yake a Roma, ya neme ni ido a rufe sai da ya same ni.
Nay, when he was here in Rome, he took great pains to inquire where I was living, and at last he found me.
18 Bari Ubangiji yă sa yă sami jinƙai daga Ubangiji a wancan ranar! Ka sani sarai yadda ya taimake ni a hanyoyi dabam-dabam a Afisa.
(The Lord grant that he may obtain mercy at His hands on that day!) And you yourself well know all the services which he rendered me in Ephesus.

< 2 Timoti 1 >