< 2 Timoti 2 >
1 Kai kuma, ɗana, ka yi ƙarfi cikin alherin da yake cikin Kiristi Yesu.
O OE hoi, e ka'u keiki, e hooikaika ma ka pono iloko o Kristo Iesu.
2 Abubuwan da ka ji na faɗa a gaban shaidu masu yawa kuwa ka danƙa wa amintattun mutane waɗanda su ma za su iya koya wa waɗansu.
A o na mea au i lohe mai ai ia'u ma na mea hoike he lehulehu, oia kau e kauoha aku ai i na kanaka kupaa, i ka poe makaukau hoi i ke ao aku ia hai.
3 Ka jure wa shan wahala tare da mu kamar soja mai kyau na Kiristi Yesu.
E hoomanawanui hoi oe me he koa maikai la no Iesu Kristo.
4 Ba wanda yake aikin soja da zai sa kansa a sha’anin mutumin da ba ya aikin soja, domin yakan so yă gamshi wanda ya ɗauke shi soja.
Aole ke kanaka kaua e hoohihia ia ia iho i na mea o keia ola ana; i hiki hoi ia ia ke hooluola i ka mea nana ia i kuka e lilo i koa.
5 Haka ma, in wani ya yi gasa a matsayi shi ɗan wasa ne, ba ya sami rawanin nasara, sai in ya yi gasar bisa ga dokoki.
Ina e paio kekahi i lanakila, aole ia e hooleiia i ka lei, ke paio ole mamuli o ke kanawai.
6 Manomi mai aiki sosai ya kamata yă zama na fari wajen samun rabon amfanin gona.
He pono no ka mahiai e hana ia mamua o ka loaa ana o ka hua.
7 Ka yi tunani a kan abin da nake faɗi, gama Ubangiji zai ba ka ganewa cikin dukan wannan.
E noonoo oe i ka'u e olelo nei; a e haawi mai ka Haku ia oe i ka naauao ma na mea a pau.
8 Ka tuna da Yesu Kiristi, wanda aka tā da shi daga matattu, zuriyar Dawuda, wanda shi ne bisharata,
E hoomanao hoi oe ia Iesu Kristo ka mamo a Davida, ua hoala hou ia mai ka make mai, e like me ka'u euanelio;
9 wadda nake shan wahala har ga daurin sarƙa kamar mai laifi. Amma Maganar Allah ba a daure take ba.
E a mea a'u i loohia'i i ka ino a me ka paa ana, me he kanaka hewa la; aka, aole i hoopeaia ka olelo a ke Akua.
10 Saboda haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton da yake cikin Kiristi Yesu, tare da madawwamiyar ɗaukaka. (aiōnios )
Nolaila au e hoomanawanui nei i na mea a pau e pono ai ka poe i alobaia, i loaa hoi ia lakou ke ola iloko o Kristo Iesu, mo ka nani mau loa. (aiōnios )
11 Ga wata magana tabbatacciya, “In muka mutu tare da shi, za mu rayu tare da shi;
He olelo oiaio keia; Ina i make pu kakou, e ola pu no hoi kakou.
12 in muka jimre, za mu yi mulki tare da shi. In muka yi mūsunsa, shi ma zai yi mūsunmu;
Ina e hoomanawanui pu kakou, e noho pu no hoi kakou i ke aupuni; a ina e hoole aku kakou ia ia, oia kekahi e hoole mai ia kakou.
13 in ba mu da aminci, shi dai mai aminci ne, domin shi ba zai iya mūsun kansa ba.”
A ina o kupaa ole kakou, oia nae ke kupaa mau; aole e hiki ia ia ke hoole ia ia iho.
14 Ka riƙa tuna masu da haka, ka kuma gama su da Allah, kada su yi jayayya a kan maganganu, don ba ta da wani amfani, sai ɓad da masu ji kawai take yi.
O keia mau mea kau e paipai aku ai ia lakou, me ke kauoha aku imua i ke alo o ka Haku, e hoopaapaa ole Lakou i na huaolelo waiwai ole, e hookahuli ana i ka poe lohe mai.
15 Ka yi iyakacin ƙoƙarinka ka gabatar da kanka a gaban Allah a matsayin wanda aka amince da shi, ma’aikaci wanda ba shi da dalilin jin kunya wanda kuma yake fassara kalmar gaskiya daidai.
E hooikaika nui oe e hoike ia oe iho imua o ke alo o ke Akua me ka hoaponoia mai, i paahana hoi aole e pono ke hilahila, e puunaue pono aku ana i ka olelo oiaio.
16 Ka yi nesa da maganganun banza na rashin tsoron Allah, gama waɗanda suka mai da hankali ga yin waɗannan za su ƙara zama marasa tsoron Allah.
E pale ae hoi i ka wawa hewa ana me ka lapuwale; e ulu ana no ia e mahuahua ai ka haihaia.
17 Koyarwarsu za tă bazu kamar ruɓaɓɓen gyambo. A cikinsu akwai Himenayus da Filetus,
E aai ana hoi ka lakou olelo me he mai aai la: o Humenaio a me Pileto kekahi o lakou.
18 waɗanda suka bauɗe daga gaskiya. Suna cewa tashin matattu ya riga ya faru, suna kuma ɓata bangaskiyar waɗansu.
A no ka olelo oiaio, ua lalau hewa laua, e olelo ana ua hala e ke alahouana; a ke hoohiolo nei i ka manaoio o kekahi poe.
19 Duk da haka, ƙaƙƙarfan tushen nan na Allah yana nan daram, an hatimce shi da wannan rubutu, “Ubangiji ya san waɗanda suke nasa,” da kuma, “Duk wanda ya bayyana yarda ga sunan Ubangiji, to, dole yă yi nesa da aikata mugunta.”
Oiaio hoi, ke kupaa mau nei ke kumu a ke Akua mai, me keia hoailona ona; Ua ike mai no ka Haku i kona poe ponoi; a, O ka mea i hoohiki i ka inoa o Kristo e haalele loa aku ia i ka hewa.
20 A babban gida akwai kayayyakin da ba na zinariya da na azurfa kaɗai ba, amma har da na katako da na yumɓu ma; waɗansu domin hidima mai daraja waɗansu kuwa domin hidima marar daraja.
A iloko o ka hale nui, aole o na ipu gula a me ke kala wale no, aka, o ka laau, a me ka lepo kekahi; no ka hanohano kekahi, no ka hanohano ole kekahi.
21 In mutum ya tsabtacce kansa daga na farkon zai zama kayan aikin hidima mai daraja, mai amfani ga Maigida, kuma shiryayye domin yin kowane aiki mai kyau.
A ina i hoomaemae ke kanaka ia ia iho ia lakou, e lilo no ia i ipu hanohano, i hoomaemaeia e pono ai ka Haku, a makaukau hoi no na hana maikai a pau.
22 Ka yi nesa da mugayen sha’awace-sha’awace na ƙuruciya, ka kuma bi adalci, bangaskiya, ƙauna da kuma salama, tare da waɗanda suke kira ga Ubangiji daga zuciya mai tsabta.
E haalele hoi i na kuko o ka wa opiopio; a e hahai mamuli o ka pono, o ka manaoio, o ke aloha, a me ka maluhia; me ka poe i kahea aku i ka Haku mai loko aku o ka naau maemae.
23 Kada wani abu yă haɗa ka da gardandamin banza da wofi, domin ka san yadda suke jawo faɗa.
A o na niele lapuwale a me ka naaupo, o kau ia e pale aku, me ka ike e aku ua hooulu lakou i ka hakaka.
24 Bai kamata bawan Ubangiji yă zama mai neman faɗa ba; a maimako, dole yă nuna alheri ga kowa, mai iya koyarwa, mai haƙuri kuma.
Aole hoi e pono i ke kanwa a ka Haku e hakaka; aka, e akahai i na mea a pau, e akamai hoi i ke ao aku, e ahonui i ke ino:
25 Waɗanda suke gāba da shi kuwa dole yă yi musu gargaɗi cikin hankali, da fata Allah zai sa su tuba su kai ga sanin gaskiya,
E ao hoohaahaa aku ana i ka poe i ku e mai; i haawi mai paha ke Akua ia lakou i ka mihi a me ka hooiaio ana i ka olelo oiaio;
26 su kuma dawo cikin hankulansu su kuɓuta daga tarkon Iblis, wanda ya sa suka zama kamammu don su aikata nufinsa.
A i hoohemo lakou ia lakou iho mai loko ae o ka upena a ka diabolo, ka poe i lawe pio ia e ia ma kona makemake.