< 2 Timoti 2 >
1 Kai kuma, ɗana, ka yi ƙarfi cikin alherin da yake cikin Kiristi Yesu.
Vahvista siis sinus, minun poikani, sen armon kautta, joka Jesuksessa Kristuksessa on.
2 Abubuwan da ka ji na faɗa a gaban shaidu masu yawa kuwa ka danƙa wa amintattun mutane waɗanda su ma za su iya koya wa waɗansu.
Ja mitä sinä olet minulta monen todistajan kautta kuullut, niin käske uskollisille ihmisille, jotka myös muita olisivat soveliaat opettamaan.
3 Ka jure wa shan wahala tare da mu kamar soja mai kyau na Kiristi Yesu.
Kärsi vaivaa niinkuin luja Jesuksen Kristuksen sotamies.
4 Ba wanda yake aikin soja da zai sa kansa a sha’anin mutumin da ba ya aikin soja, domin yakan so yă gamshi wanda ya ɗauke shi soja.
Ei yksikään sotamies sekoita itsiänsä elatuksen menoihin, sille kelvataksensa, joka hänen sotaan ottanut on.
5 Haka ma, in wani ya yi gasa a matsayi shi ɗan wasa ne, ba ya sami rawanin nasara, sai in ya yi gasar bisa ga dokoki.
Ja jos joku kilvoittelee, niin ei hän kruunata, ellei hän toimellisesti kilvoittele.
6 Manomi mai aiki sosai ya kamata yă zama na fari wajen samun rabon amfanin gona.
Peltomiehen, joka pellon rakentaa, pitää ensin hedelmästä nautitseman.
7 Ka yi tunani a kan abin da nake faɗi, gama Ubangiji zai ba ka ganewa cikin dukan wannan.
Ymmärrä, mitä minä sanon: Herra antakoon sinulle ymmärryksen kaikissa;
8 Ka tuna da Yesu Kiristi, wanda aka tā da shi daga matattu, zuriyar Dawuda, wanda shi ne bisharata,
Muista Jesuksen Kristuksen päälle, joka kuolleista noussut on: Davidin siemenestä minun evankeliumini jälkeen,
9 wadda nake shan wahala har ga daurin sarƙa kamar mai laifi. Amma Maganar Allah ba a daure take ba.
Jossa minä vaivaa kärsin kahleisiin asti niinkuin pahantekiä; vaan ei Jumalan sana ole sidottu.
10 Saboda haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton da yake cikin Kiristi Yesu, tare da madawwamiyar ɗaukaka. (aiōnios )
Sentähden minä kärsin kaikki valittuin tähden, että hekin saisivat Jesuksessa Kristuksessa autuuden, ijankaikkisen kunnian kanssa. (aiōnios )
11 Ga wata magana tabbatacciya, “In muka mutu tare da shi, za mu rayu tare da shi;
Se on totinen sana: jos me ynnä olemme kuolleet, niin me myös ynnä elämme;
12 in muka jimre, za mu yi mulki tare da shi. In muka yi mūsunsa, shi ma zai yi mūsunmu;
Jos me kärsimme, niin me myös ynnä hallitsemme; jos me hänen kiellämme, niin hän meidätkin kieltää;
13 in ba mu da aminci, shi dai mai aminci ne, domin shi ba zai iya mūsun kansa ba.”
Ellemme usko, niin hän pysyy kuitenkin uskollisena, joka ei itsiänsä kieltää taida.
14 Ka riƙa tuna masu da haka, ka kuma gama su da Allah, kada su yi jayayya a kan maganganu, don ba ta da wani amfani, sai ɓad da masu ji kawai take yi.
Näitä neuvo ja todista Herran edessä, ettei he sanoista riitelisi, joka ei mihinkään kelpaa, vaan ainoastaan luovuttamaan niitä jotka kuulevat.
15 Ka yi iyakacin ƙoƙarinka ka gabatar da kanka a gaban Allah a matsayin wanda aka amince da shi, ma’aikaci wanda ba shi da dalilin jin kunya wanda kuma yake fassara kalmar gaskiya daidai.
Pyydä itses Jumalalle osoittaa toimelliseksi ja laittamattomaksi työntekijäksi, joka oikein totuuden sanan jakaa.
16 Ka yi nesa da maganganun banza na rashin tsoron Allah, gama waɗanda suka mai da hankali ga yin waɗannan za su ƙara zama marasa tsoron Allah.
Mutta siivottomat ja kelvottomat sanat hylkää, jotka paljon jumalatointa menoa saattavat.
17 Koyarwarsu za tă bazu kamar ruɓaɓɓen gyambo. A cikinsu akwai Himenayus da Filetus,
Ja heidän puheensa syö ympäriltänsä niinkuin ruumiin mato; joista on Hymeneus ja Philetus,
18 waɗanda suka bauɗe daga gaskiya. Suna cewa tashin matattu ya riga ya faru, suna kuma ɓata bangaskiyar waɗansu.
Jotka totuudesta ovat erehtyneet, sanoen ylösnousemisen jo tapahtuneen, ja ovat muutamat uskosta kääntäneet.
19 Duk da haka, ƙaƙƙarfan tushen nan na Allah yana nan daram, an hatimce shi da wannan rubutu, “Ubangiji ya san waɗanda suke nasa,” da kuma, “Duk wanda ya bayyana yarda ga sunan Ubangiji, to, dole yă yi nesa da aikata mugunta.”
Mutta Jumalan vahva perustus kuitenkin pysyy, joka tällä kiinnitetty on: Herra tuntee omansa: ja lakatkaan jokainen vääryydestä, joka Kristuksen nimeä mainitsee.
20 A babban gida akwai kayayyakin da ba na zinariya da na azurfa kaɗai ba, amma har da na katako da na yumɓu ma; waɗansu domin hidima mai daraja waɗansu kuwa domin hidima marar daraja.
Mutta suuressa huoneessa ei ole ainoastaan kultaiset ja hopiaiset astiat, vaan myös puiset ja saviset, ja muutamat tosin kunniaksi, mutta muutamat häpiäksi.
21 In mutum ya tsabtacce kansa daga na farkon zai zama kayan aikin hidima mai daraja, mai amfani ga Maigida, kuma shiryayye domin yin kowane aiki mai kyau.
Jos joku itsensä senkaltaisista ihmisistä puhdistaa, se tulee kunniaan pyhitetyksi astiaksi, perheenisännälle tarpeelliseksi ja kaikkiin hyviin töihin valmistetuksi.
22 Ka yi nesa da mugayen sha’awace-sha’awace na ƙuruciya, ka kuma bi adalci, bangaskiya, ƙauna da kuma salama, tare da waɗanda suke kira ga Ubangiji daga zuciya mai tsabta.
Nuoruuden himot vältä; mutta noudata vanhurskautta, uskoa, rakkautta ja rauhaa kaikkein niiden kanssa, jotka puhtaasta sydämestä Herraa rukoilevat.
23 Kada wani abu yă haɗa ka da gardandamin banza da wofi, domin ka san yadda suke jawo faɗa.
Hullut ja turhat kysymykset hylkää, tietäen, että ne ainoastaan riidat synnyttävät.
24 Bai kamata bawan Ubangiji yă zama mai neman faɗa ba; a maimako, dole yă nuna alheri ga kowa, mai iya koyarwa, mai haƙuri kuma.
Mutta ei Herran palvelian tule riitaisen olla, vaan siviän jokaista kohtaan, opettavaisen, pahoja kärsiväisen.
25 Waɗanda suke gāba da shi kuwa dole yă yi musu gargaɗi cikin hankali, da fata Allah zai sa su tuba su kai ga sanin gaskiya,
Hiljaisuudessa nuhtelevaisen vastahakoisia; jos Jumala heille joskus antais parannuksen totuutta ymmärtämään,
26 su kuma dawo cikin hankulansu su kuɓuta daga tarkon Iblis, wanda ya sa suka zama kamammu don su aikata nufinsa.
Ja he jälleen katuisivat ja perkeleen paulasta pääsisivät, jolta he hänen tahtonsa jälkeen vangitut ovat.