< 2 Timoti 2 >
1 Kai kuma, ɗana, ka yi ƙarfi cikin alherin da yake cikin Kiristi Yesu.
You then, my child, must be strong in the grace that is in Christ Jesus.
2 Abubuwan da ka ji na faɗa a gaban shaidu masu yawa kuwa ka danƙa wa amintattun mutane waɗanda su ma za su iya koya wa waɗansu.
All that you have been taught by me in the hearing of many witnesses, you must hand on to trusty men who shall themselves, in turn, be competent to instruct others also.
3 Ka jure wa shan wahala tare da mu kamar soja mai kyau na Kiristi Yesu.
As a good soldier of Christ Jesus accept your share of suffering.
4 Ba wanda yake aikin soja da zai sa kansa a sha’anin mutumin da ba ya aikin soja, domin yakan so yă gamshi wanda ya ɗauke shi soja.
Every one who serves as a soldier keeps himself from becoming entangled in the world's business--so that he may satisfy the officer who enlisted him.
5 Haka ma, in wani ya yi gasa a matsayi shi ɗan wasa ne, ba ya sami rawanin nasara, sai in ya yi gasar bisa ga dokoki.
And if any one takes part in an athletic contest, he gets no prize unless he obeys the rules.
6 Manomi mai aiki sosai ya kamata yă zama na fari wajen samun rabon amfanin gona.
The harvestman who labours in the field must be the first to get a share of the crop.
7 Ka yi tunani a kan abin da nake faɗi, gama Ubangiji zai ba ka ganewa cikin dukan wannan.
Mark well what I am saying: the Lord will give you discernment in everything.
8 Ka tuna da Yesu Kiristi, wanda aka tā da shi daga matattu, zuriyar Dawuda, wanda shi ne bisharata,
Never forget that Jesus Christ has risen from among the dead and is a descendant of David, as is declared in the Good News which I preach.
9 wadda nake shan wahala har ga daurin sarƙa kamar mai laifi. Amma Maganar Allah ba a daure take ba.
For preaching the Good News I suffer, and am even put in chains, as if I were a criminal: yet the word of God is not imprisoned.
10 Saboda haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton da yake cikin Kiristi Yesu, tare da madawwamiyar ɗaukaka. (aiōnios )
For this reason I endure all things for the sake of God's own people; so that they also may obtain salvation--even the salvation which is in Christ Jesus--and with it eternal glory. (aiōnios )
11 Ga wata magana tabbatacciya, “In muka mutu tare da shi, za mu rayu tare da shi;
Faithful is the saying: "If we died with Him, we shall also live with Him;
12 in muka jimre, za mu yi mulki tare da shi. In muka yi mūsunsa, shi ma zai yi mūsunmu;
"If we patiently endure pain, we shall also share His Kingship; "If we disown Him, He will also disown us;
13 in ba mu da aminci, shi dai mai aminci ne, domin shi ba zai iya mūsun kansa ba.”
"And even if our faith fails, He remains true--He cannot prove false to Himself."
14 Ka riƙa tuna masu da haka, ka kuma gama su da Allah, kada su yi jayayya a kan maganganu, don ba ta da wani amfani, sai ɓad da masu ji kawai take yi.
Bring all this to men's remembrances, solemnly charging them in the presence of God not to waste time in wrangling about mere words, a course which is altogether unprofitable and tends only to the ruin of the hearers.
15 Ka yi iyakacin ƙoƙarinka ka gabatar da kanka a gaban Allah a matsayin wanda aka amince da shi, ma’aikaci wanda ba shi da dalilin jin kunya wanda kuma yake fassara kalmar gaskiya daidai.
Earnestly seek to commend yourself to God as a servant who, because of his straightforward dealing with the word of truth, has no reason to feel any shame.
16 Ka yi nesa da maganganun banza na rashin tsoron Allah, gama waɗanda suka mai da hankali ga yin waɗannan za su ƙara zama marasa tsoron Allah.
But from irreligious and frivolous talk hold aloof, for those who indulge in it will proceed from bad to worse in impiety,
17 Koyarwarsu za tă bazu kamar ruɓaɓɓen gyambo. A cikinsu akwai Himenayus da Filetus,
and their teaching will spread like a running sore. Hymenaeus and Philetus are men of that stamp.
18 waɗanda suka bauɗe daga gaskiya. Suna cewa tashin matattu ya riga ya faru, suna kuma ɓata bangaskiyar waɗansu.
In the matter of the truth they have gone astray, saying that the Resurrection is already past, and so they are overthrowing the faith of some.
19 Duk da haka, ƙaƙƙarfan tushen nan na Allah yana nan daram, an hatimce shi da wannan rubutu, “Ubangiji ya san waɗanda suke nasa,” da kuma, “Duk wanda ya bayyana yarda ga sunan Ubangiji, to, dole yă yi nesa da aikata mugunta.”
Yet God's solid foundation stands unmoved, bearing this inscription, "The Lord knows those who really belong to Him." And this also, "Let every one who names the Name of the Lord renounce all wickedness."
20 A babban gida akwai kayayyakin da ba na zinariya da na azurfa kaɗai ba, amma har da na katako da na yumɓu ma; waɗansu domin hidima mai daraja waɗansu kuwa domin hidima marar daraja.
Now in a great house there are not only articles of gold and silver, but also others of wood and of earthenware; and some are for specially honourable, and others for common use.
21 In mutum ya tsabtacce kansa daga na farkon zai zama kayan aikin hidima mai daraja, mai amfani ga Maigida, kuma shiryayye domin yin kowane aiki mai kyau.
If therefore a man keeps himself clear of these latter, he himself will be for specially honourable use, consecrated, fit for the Master's service, and fully equipped for every good work.
22 Ka yi nesa da mugayen sha’awace-sha’awace na ƙuruciya, ka kuma bi adalci, bangaskiya, ƙauna da kuma salama, tare da waɗanda suke kira ga Ubangiji daga zuciya mai tsabta.
Keep a strong curb, however, on your youthful cravings; and strive for integrity, good faith, love, peace, in company with all who pray to the Lord with pure hearts.
23 Kada wani abu yă haɗa ka da gardandamin banza da wofi, domin ka san yadda suke jawo faɗa.
But avoid foolish discussions with ignorant men, knowing--as you do--that these lead to quarrels;
24 Bai kamata bawan Ubangiji yă zama mai neman faɗa ba; a maimako, dole yă nuna alheri ga kowa, mai iya koyarwa, mai haƙuri kuma.
and a bondservant of the Lord must not quarrel, but must be inoffensive towards all men, a skilful teacher, and patient under wrongs.
25 Waɗanda suke gāba da shi kuwa dole yă yi musu gargaɗi cikin hankali, da fata Allah zai sa su tuba su kai ga sanin gaskiya,
He must speak in a gentle tone when correcting the errors of opponents, in the hope that God will at last give them repentance, for them to come to a full knowledge of the truth
26 su kuma dawo cikin hankulansu su kuɓuta daga tarkon Iblis, wanda ya sa suka zama kamammu don su aikata nufinsa.
and recover sober-mindedness and freedom from the Devil's snare, though they are now entrapped by him to do his will.