< 2 Tessalonikawa 1 >

1 Bulus, da Sila, da Timoti, Zuwa ga ikkilisiya ta Tessalonikawa ta Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi.
Paul, Silvanus et Timothée à l'église des Thessaloniciens en Dieu notre Père et en Jésus-Christ le Seigneur.
2 Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grâce et paix vous soient accordées par Dieu notre Père et par le Seigneur Jésus-Christ
3 Dole kullum mu gode wa Allah saboda ku,’yan’uwa, haka kuwa ya dace, domin bangaskiyarku tana girma gaba-gaba, ƙaunar da kowannenku yake yi wa juna kuwa tana ƙaruwa.
Nous devons sans cesse rendre grâces à Dieu à votre sujet; frères, ce n'est que juste, car votre foi s'accroît beaucoup, et votre amour les uns pour les autres augmente tellement que
4 Saboda haka, a cikin ikkilisiyoyin Allah muna taƙama game da daurewarku da kuma bangaskiyarku cikin dukan tsanani da gwaje-gwajen da kuke sha.
nous nous félicitons de vous auprès des Églises de Dieu; nous leur parlons de votre patience et de votre foi dans toutes les persécutions et les afflictions que vous avez eues à supporter.
5 Dukan wannan yana tabbatar cewa hukuncin Allah daidai ne, saboda haka kuma za a lissafta ku a kan kun cancanci mulkin Allah, wanda dominsa ne kuke shan wahala.
Il y a là comme un présage du juste jugement de Dieu; un jour vous serez jugés dignes de son Royaume pour lequel vous souffrez.
6 Allah mai adalci ne, Zai sāka wa masu ba ku wahala da wahala
Car enfin il est juste devant Dieu qu'il fasse souffrir à leur tour ceux qui vous font souffrir,
7 yă kuma sauƙaƙa muku ku da kuke wahala, har ma da mu. Wannan zai faru sa’ad da aka bayyana Ubangiji Yesu daga sama cikin wuta mai ci tare da mala’ikunsa masu iko.
et qu'il vous donne du repos avec nous à vous qui souffrez. Cela sera quand le Seigneur Jésus descendra du ciel avec les anges de sa puissance;
8 Zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da kuma waɗanda ba su yi biyayya da bisharar Ubangijinmu Yesu ba.
«Entouré de flammes de feu, il fera justice» de ceux qui méconnaissent Dieu et qui n'obéissent pas à l'Évangile de notre Seigneur Jésus.
9 Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios g166)
Leur châtiment sera la destruction éternelle, «Loin de la face du Seigneur Et de son éclatante puissance», (aiōnios g166)
10 a ranar da zai dawo don a ɗaukaka shi a cikin mutanensa masu tsarki, yă kuma zama abin banmamaki ga dukan waɗanda suka gaskata. Wannan ya haɗa har da ku, domin kun gaskata shaidar da muka yi muku.
quand il viendra pour être, en ce jour-là, glorifié au milieu de ses fidèles et admiré par tous ceux qui auront été croyants; car vous avez cru à notre témoignage.
11 Sane da wannan, kullum muna addu’a saboda ku, don Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ta wurin ikonsa kuma yă cika kowace manufarku mai kyau da kuma kowane aikin da bangaskiyarku ta iza.
Voilà aussi pourquoi nous prions sans cesse pour vous; nous demandons que notre Dieu vous trouve dignes de son appel; qu'il vous remplisse, dans sa puissance, de bonnes dispositions et d'oeuvres de foi.
12 Muna wannan addu’a don sunan Ubangijinmu Yesu yă sami ɗaukaka a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu da na Ubangiji Yesu Kiristi.
C'est ainsi que le nom de notre Seigneur Jésus-Christ sera glorifié en vous, et vous en lui, par la grâce de notre Dieu et du Seigneur Jésus-Christ.

< 2 Tessalonikawa 1 >