< 2 Tessalonikawa 1 >
1 Bulus, da Sila, da Timoti, Zuwa ga ikkilisiya ta Tessalonikawa ta Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi.
PAUL and Sylvanus and Timothy, to the church of the Thessalonians, which is in God our Father and our Lord Jesus the Messiah:
2 Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grace be with you, and peace, from God our Father, and from our Lord Jesus the Messiah.
3 Dole kullum mu gode wa Allah saboda ku,’yan’uwa, haka kuwa ya dace, domin bangaskiyarku tana girma gaba-gaba, ƙaunar da kowannenku yake yi wa juna kuwa tana ƙaruwa.
We are bound to give thanks to God always, on your account, my brethren, as it is proper; because your faith groweth exceedingly, and, in you all, the love of each for his fellow increaseth.
4 Saboda haka, a cikin ikkilisiyoyin Allah muna taƙama game da daurewarku da kuma bangaskiyarku cikin dukan tsanani da gwaje-gwajen da kuke sha.
Insomuch that we also boast of you in the churches of God, on account of your faith, and your patience in all the persecution and trials that ye endure;
5 Dukan wannan yana tabbatar cewa hukuncin Allah daidai ne, saboda haka kuma za a lissafta ku a kan kun cancanci mulkin Allah, wanda dominsa ne kuke shan wahala.
for a demonstration of the righteous judgment of God; that ye may be worthy of his kingdom, on account of which ye suffer.
6 Allah mai adalci ne, Zai sāka wa masu ba ku wahala da wahala
And since it is a righteous thing with God, to recompense trouble to them that trouble you:
7 yă kuma sauƙaƙa muku ku da kuke wahala, har ma da mu. Wannan zai faru sa’ad da aka bayyana Ubangiji Yesu daga sama cikin wuta mai ci tare da mala’ikunsa masu iko.
and you, who are the troubled, he will vivify, with us, at the manifestation of our Lord Jesus the Messiah from heaven, with the host of his angels;
8 Zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da kuma waɗanda ba su yi biyayya da bisharar Ubangijinmu Yesu ba.
when he will execute vengeance, with the burning of fire, on them that know not God, and on them that acknowledge not the gospel of our Lord Jesus the Messiah.
9 Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios )
For these will be recompensed with the judgment of eternal destruction, from the presence of our Lord, and from the glory of his power; (aiōnios )
10 a ranar da zai dawo don a ɗaukaka shi a cikin mutanensa masu tsarki, yă kuma zama abin banmamaki ga dukan waɗanda suka gaskata. Wannan ya haɗa har da ku, domin kun gaskata shaidar da muka yi muku.
when he shall come to be glorified in his saints, and to display his wonders in his faithful ones; for our testimony concerning you, will be believed, in that day.
11 Sane da wannan, kullum muna addu’a saboda ku, don Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ta wurin ikonsa kuma yă cika kowace manufarku mai kyau da kuma kowane aikin da bangaskiyarku ta iza.
Therefore we pray for you, at all times; that God would make you worthy of your calling, and would fill you with all readiness for good deeds, and with the works of faith by power;
12 Muna wannan addu’a don sunan Ubangijinmu Yesu yă sami ɗaukaka a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu da na Ubangiji Yesu Kiristi.
so that the name of our Lord Jesus the Messiah, may be glorified in you, (and) ye also in him; according to the grace of God, and of our Lord Jesus the Messiah.