< 2 Tessalonikawa 3 >

1 A ƙarshe,’yan’uwa, ku yi mana addu’a domin saƙon Ubangiji yă yi saurin bazuwa a kuma girmama shi, kamar yadda yake a wurinku.
Henceforth, brethren, pray ye for us, that the word of our Lord may, in every place, run and be glorified, as with you;
2 Ku kuma yi addu’a yadda za a cece mu daga mugayen mutane masu mugunta, gama ba kowa ba ne yake da bangaskiya.
and that we may be delivered from evil and perverse men; for faith is not in all.
3 Ubangiji mai aminci ne, zai ƙarfafa ku, yă kuma tsare ku daga mugun nan.
And faithful is the Lord, who will keep you and rescue you from the evil One.
4 Muna da tabbaci cikin Ubangiji cewa kuna bin umarnai da muka yi muku, za ku kuma ci gaba da yin abubuwan da muka umarta.
And we have confidence in you, through our Lord, that what we have inculcated on you, ye both have done, and will do.
5 Bari Ubangiji yă bi da zukatanku ga ƙaunan nan ta Allah da kuma jimirin nan na Kiristi.
And may our Lord direct your hearts to the love of God, and to a patient waiting for the Messiah.
6 A cikin sunan Ubangiji Yesu Kiristi, muna muku umarni,’yan’uwa, da ku kiyaye kanku daga kowane ɗan’uwa mai zaman banza da ba ya rayuwa bisa ga koyarwar da kuka karɓa daga wurinmu.
And we enjoin upon you, my brethren, in the name of our Lord Jesus the Messiah, that ye withdraw from every brother who walketh wickedly, and not according to the precepts which ye received from us.
7 Gama ku kanku kun san yadda ya kamata ku bi gurbinmu. Ba mu yi zaman banza sa’ad da muke tare da ku ba,
For ye know how ye ought to imitate us, who did not walk wickedly among you.
8 ba mu kuwa ci abincin kowa ba tare da ba mu biya ba. A maimakon haka, mun yi aiki dare da rana, muna fama muna wahala kuma don kada mu nawaita wa waninku.
Neither did we eat bread gratuitously from any of you; but, with toil and weariness, we labored by night and by day, that we might not be burdensome to any of you.
9 Mun yi wannan, ba don ba mu da’yancin karɓar irin taimakon nan ba ne, sai dai domin mu zama gurbin da za ku bi.
It was not because we have no authority, but that we might give you an example in ourselves, that ye might imitate us.
10 Ko ma a sa’ad da muke tare da ku, mun ba ku wannan umarni cewa, “In mutum ya ƙi yin aiki, kada a ba shi abinci.”
And while we were with you, we also gave you this precept, That every one who would not work, should likewise not eat.
11 Mun ji cewa waɗansunku suna zaman banza. Ba sa aikin kome; sai shisshigi kurum.
For we hear, there are some among you who walk wickedly, and do nothing except vain things.
12 Irin waɗannan mutane muna ba da umarni muna kuma gargaɗe su cikin Ubangiji Yesu Kiristi su natsu su kuma nemi abincin da suke ci.
Now such persons, we command and exhort, by our Lord Jesus the Messiah, that in quietness they work, and eat their own bread.
13 Game da ku kuma’yan’uwa, kada ku gaji da yin abin da yake daidai.
And my brethren, let it not be wearisome to you, to do what is good.
14 In wani bai yi biyayya da umarninmu a wannan wasiƙa ba, sai fa ku lura da shi. Kada ku haɗa kai da shi, don yă ji kunya.
And if any one hearkeneth not to these my words in this epistle, separate that man from you, and have no intimacy with him, that he may be ashamed.
15 Duk da haka kada ku mai da shi abokin gāba, sai dai ku gargaɗe shi a matsayin ɗan’uwa.
Yet, hold him not as an enemy, but admonish him as a brother.
16 Yanzu, bari Ubangiji mai salama kansa yă ba ku salama a kowane lokaci da kuma a ta kowace hanya. Ubangiji yă kasance tare da ku duka.
And may the Lord of peace give you peace, always, in every thing. Our Lord be with you all.
17 Ni, Bulus, nake rubuta wannan gaisuwa da hannuna, wannan ce shaida a kowace wasiƙata, haka nake rubutu.
The salutation in the writing of my own hand, I Paul have written it; which is the token in all my epistles, so I write.
18 Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ku duka.
The grace of Jesus the Messiah be with you all, my brethren. Amen.

< 2 Tessalonikawa 3 >