< 2 Tessalonikawa 1 >

1 Bulus, da Sila, da Timoti, Zuwa ga ikkilisiya ta Tessalonikawa ta Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi.
Paul and Silvanus and Timothy to the church of the Thessalonians in God our Father, and in the Lord Jesus Christ;
2 Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
grace be to you and peace from God our Father, and from the Lord Jesus Christ.
3 Dole kullum mu gode wa Allah saboda ku,’yan’uwa, haka kuwa ya dace, domin bangaskiyarku tana girma gaba-gaba, ƙaunar da kowannenku yake yi wa juna kuwa tana ƙaruwa.
We ought always to give thanks to God on your account, my brethren, as it is fit; because your faith increaseth greatly, and the love of every one of you towards each other aboundeth:
4 Saboda haka, a cikin ikkilisiyoyin Allah muna taƙama game da daurewarku da kuma bangaskiyarku cikin dukan tsanani da gwaje-gwajen da kuke sha.
so that we ourselves boast of you among the churches of God, for your patience and faith under all your persecutions and afflictions which ye endure.
5 Dukan wannan yana tabbatar cewa hukuncin Allah daidai ne, saboda haka kuma za a lissafta ku a kan kun cancanci mulkin Allah, wanda dominsa ne kuke shan wahala.
Which are a demonstration of the just judgement of God, that ye may be counted worthy of the kingdom of God, for which ye also suffer:
6 Allah mai adalci ne, Zai sāka wa masu ba ku wahala da wahala
seeing it is a righteous thing with God to render affliction to those that afflict you;
7 yă kuma sauƙaƙa muku ku da kuke wahala, har ma da mu. Wannan zai faru sa’ad da aka bayyana Ubangiji Yesu daga sama cikin wuta mai ci tare da mala’ikunsa masu iko.
and to you, who are in trouble, rest with us, at the revelation of the Lord Jesus from heaven,
8 Zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da kuma waɗanda ba su yi biyayya da bisharar Ubangijinmu Yesu ba.
with his mighty angels, in flaming fire, taking vengeance on those who know not God, and who obey not the gospel of our Lord Jesus Christ:
9 Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios g166)
who shall be punished with everlasting destruction, by the presence of the Lord and by his glorious power: (aiōnios g166)
10 a ranar da zai dawo don a ɗaukaka shi a cikin mutanensa masu tsarki, yă kuma zama abin banmamaki ga dukan waɗanda suka gaskata. Wannan ya haɗa har da ku, domin kun gaskata shaidar da muka yi muku.
in that day, when He shall come to be glorified in his saints, and to be admired in all them that believe; because our testimony among you was believed.
11 Sane da wannan, kullum muna addu’a saboda ku, don Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ta wurin ikonsa kuma yă cika kowace manufarku mai kyau da kuma kowane aikin da bangaskiyarku ta iza.
Wherefore we pray always for you, that our God would count you worthy of this calling, and fulfil all the good pleasure of his goodness, and the work of faith with power:
12 Muna wannan addu’a don sunan Ubangijinmu Yesu yă sami ɗaukaka a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu da na Ubangiji Yesu Kiristi.
that the name of our Lord Jesus Christ may be glorified in you, and ye in Him, according to the grace of our God, and of the Lord Jesus Christ.

< 2 Tessalonikawa 1 >