< 2 Tessalonikawa 1 >

1 Bulus, da Sila, da Timoti, Zuwa ga ikkilisiya ta Tessalonikawa ta Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi.
Paul, Silas, and Timothy: To the Church of the Thessalonians which is in God our Father and the Lord Jesus Christ.
2 Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
May grace and peace be granted to you from God our Father and the Lord Jesus Christ.
3 Dole kullum mu gode wa Allah saboda ku,’yan’uwa, haka kuwa ya dace, domin bangaskiyarku tana girma gaba-gaba, ƙaunar da kowannenku yake yi wa juna kuwa tana ƙaruwa.
Unceasing thanks are due from us to God on your behalf, brethren. They are appropriate because your faith is growing greatly, and the love of every one of you for all the others goes on increasing.
4 Saboda haka, a cikin ikkilisiyoyin Allah muna taƙama game da daurewarku da kuma bangaskiyarku cikin dukan tsanani da gwaje-gwajen da kuke sha.
It so increases that we ourselves make honourable mention of you among the Churches of God because of your patience and faith amid all your persecutions and amid the afflictions which you are enduring.
5 Dukan wannan yana tabbatar cewa hukuncin Allah daidai ne, saboda haka kuma za a lissafta ku a kan kun cancanci mulkin Allah, wanda dominsa ne kuke shan wahala.
For these are a plain token of God's righteous judgement, which has in view your being deemed worthy of admission to God's Kingdom, for the sake of which, indeed, you are sufferers.
6 Allah mai adalci ne, Zai sāka wa masu ba ku wahala da wahala
A plain token of God's righteous judgement, I say, since it is a righteous thing for Him to requite with affliction those who are now afflicting you;
7 yă kuma sauƙaƙa muku ku da kuke wahala, har ma da mu. Wannan zai faru sa’ad da aka bayyana Ubangiji Yesu daga sama cikin wuta mai ci tare da mala’ikunsa masu iko.
and to requite with rest you who are suffering affliction now--rest with us at the re-appearing of the Lord Jesus from Heaven, attended by His mighty angels.
8 Zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da kuma waɗanda ba su yi biyayya da bisharar Ubangijinmu Yesu ba.
He will come in flames of fire to take vengeance on those who have no knowledge of God, and do not obey the Good News as to Jesus, our Lord.
9 Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios g166)
They will pay the penalty of eternal destruction, being banished from the presence of the Lord and from His glorious majesty, (aiōnios g166)
10 a ranar da zai dawo don a ɗaukaka shi a cikin mutanensa masu tsarki, yă kuma zama abin banmamaki ga dukan waɗanda suka gaskata. Wannan ya haɗa har da ku, domin kun gaskata shaidar da muka yi muku.
when He comes on that day to be glorified in His people and to be wondered at among all who have believed, including you--because you believed the testimony which we brought for your acceptance.
11 Sane da wannan, kullum muna addu’a saboda ku, don Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ta wurin ikonsa kuma yă cika kowace manufarku mai kyau da kuma kowane aikin da bangaskiyarku ta iza.
It is with this view also that we continually pray to our God for you, asking that He will count you worthy of His call, and by His mighty power fully gratify your every desire for what is truly good and make your work of faith complete;
12 Muna wannan addu’a don sunan Ubangijinmu Yesu yă sami ɗaukaka a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu da na Ubangiji Yesu Kiristi.
in order that the name of our Lord Jesus may be glorified in you, and that you may be glorified in Him--so wonderful is the grace of our God and of the Lord Jesus Christ!

< 2 Tessalonikawa 1 >