< 2 Tessalonikawa 1 >

1 Bulus, da Sila, da Timoti, Zuwa ga ikkilisiya ta Tessalonikawa ta Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi.
PAULOS, and Sylvanos, and Timotheos, to the church of the Thesalonikoyee, which is in Aloha our Father, and our Lord Jeshu Meshiha.
2 Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grace be with you, and peace, from Aloha our Father, and from our Lord Jeshu Meshiha.
3 Dole kullum mu gode wa Allah saboda ku,’yan’uwa, haka kuwa ya dace, domin bangaskiyarku tana girma gaba-gaba, ƙaunar da kowannenku yake yi wa juna kuwa tana ƙaruwa.
To give thanks we owe to Aloha at all time on behalf of you, my brethren, as it is proper; because your faith greatly increaseth, and the love of you all, of every man toward his neighbour, enlargeth;
4 Saboda haka, a cikin ikkilisiyoyin Allah muna taƙama game da daurewarku da kuma bangaskiyarku cikin dukan tsanani da gwaje-gwajen da kuke sha.
as that we also boast of you in the churches of Aloha, of your faith and of your patience, in all your persecution and your affliction which you endure;
5 Dukan wannan yana tabbatar cewa hukuncin Allah daidai ne, saboda haka kuma za a lissafta ku a kan kun cancanci mulkin Allah, wanda dominsa ne kuke shan wahala.
for a demonstration of the just judgment of Aloha, that you may be worthy of his kingdom, for the sake of which you suffer;
6 Allah mai adalci ne, Zai sāka wa masu ba ku wahala da wahala
and whether it is (not) righteous to render afflictions to them who afflict you.
7 yă kuma sauƙaƙa muku ku da kuke wahala, har ma da mu. Wannan zai faru sa’ad da aka bayyana Ubangiji Yesu daga sama cikin wuta mai ci tare da mala’ikunsa masu iko.
And you who are afflicted will he save with us, at the revelation of our Lord Jeshu Meshiha from heaven, with the host Of his angels, when he executeth the punishment, with burning of fire,
8 Zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da kuma waɗanda ba su yi biyayya da bisharar Ubangijinmu Yesu ba.
on them who have not known Aloha, and on them who have not acknowledged the gospel of our Lord Jeshu Meshiha.
9 Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios g166)
For these in the judgment will be punished (with) the perdition of eternity, from the presence of our Lord, and from the glory of his power; (aiōnios g166)
10 a ranar da zai dawo don a ɗaukaka shi a cikin mutanensa masu tsarki, yă kuma zama abin banmamaki ga dukan waɗanda suka gaskata. Wannan ya haɗa har da ku, domin kun gaskata shaidar da muka yi muku.
when he cometh to be glorified in his saints, and to show his wonders in his faithful ones, that our testimony that was concerning you may be believed in that day.
11 Sane da wannan, kullum muna addu’a saboda ku, don Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ta wurin ikonsa kuma yă cika kowace manufarku mai kyau da kuma kowane aikin da bangaskiyarku ta iza.
On account of this at all time pray we for you, that Aloha may make you meet for your calling, and complete in you all the will of good (things), and the operations of faith with power;
12 Muna wannan addu’a don sunan Ubangijinmu Yesu yă sami ɗaukaka a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu da na Ubangiji Yesu Kiristi.
that the name of our Lord Jeshu Meshiha may be glorified in you, and you also in him, according to the grace of Aloha and our Lord Jeshu Meshiha.

< 2 Tessalonikawa 1 >