< 2 Tessalonikawa 1 >

1 Bulus, da Sila, da Timoti, Zuwa ga ikkilisiya ta Tessalonikawa ta Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi.
This letter comes from Paul, Silvanus, and Timothy to the church of the Thessalonians who belong to God our Father and the Lord Jesus Christ.
2 Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
May you have grace and peace from God the Father and the Lord Jesus Christ.
3 Dole kullum mu gode wa Allah saboda ku,’yan’uwa, haka kuwa ya dace, domin bangaskiyarku tana girma gaba-gaba, ƙaunar da kowannenku yake yi wa juna kuwa tana ƙaruwa.
We keep on thanking God for you, brothers and sisters—we just have to! This is the right thing to do because your trust in God is growing in leaps and bounds, and the love you all have for each other increases more and more.
4 Saboda haka, a cikin ikkilisiyoyin Allah muna taƙama game da daurewarku da kuma bangaskiyarku cikin dukan tsanani da gwaje-gwajen da kuke sha.
We speak so proudly of you among the churches of God because of your patient courage and trust in God during all the persecution and trouble you're going through.
5 Dukan wannan yana tabbatar cewa hukuncin Allah daidai ne, saboda haka kuma za a lissafta ku a kan kun cancanci mulkin Allah, wanda dominsa ne kuke shan wahala.
For this is evidence that God is right in the decisions he makes, and that you deserve the kingdom of God for which you are suffering.
6 Allah mai adalci ne, Zai sāka wa masu ba ku wahala da wahala
Since God does what's right he will deal appropriately with those who cause you trouble.
7 yă kuma sauƙaƙa muku ku da kuke wahala, har ma da mu. Wannan zai faru sa’ad da aka bayyana Ubangiji Yesu daga sama cikin wuta mai ci tare da mala’ikunsa masu iko.
He will free you from your suffering—and us too—when the Lord Jesus appears from heaven in blazing fire with his powerful angels,
8 Zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da kuma waɗanda ba su yi biyayya da bisharar Ubangijinmu Yesu ba.
bringing judgment on those who reject God and refuse to accept the good news of our Lord Jesus.
9 Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios g166)
They will rightly experience the consequence of eternal loss, separated from the presence of the Lord and his glorious power, (aiōnios g166)
10 a ranar da zai dawo don a ɗaukaka shi a cikin mutanensa masu tsarki, yă kuma zama abin banmamaki ga dukan waɗanda suka gaskata. Wannan ya haɗa har da ku, domin kun gaskata shaidar da muka yi muku.
on the day when he comes to receive glory from his people, admired by all those who trust in him. This includes you because you were convinced about what we told you.
11 Sane da wannan, kullum muna addu’a saboda ku, don Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ta wurin ikonsa kuma yă cika kowace manufarku mai kyau da kuma kowane aikin da bangaskiyarku ta iza.
That's why we continue to pray for you, that our God may make you worthy of what he's called us to do. May God powerfully fulfill every desire you have to do good and every action that comes from trusting him
12 Muna wannan addu’a don sunan Ubangijinmu Yesu yă sami ɗaukaka a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu da na Ubangiji Yesu Kiristi.
so that the name of our Lord Jesus may be honored by what you do—and in turn you are honored by him through the grace of our God and the Lord Jesus Christ.

< 2 Tessalonikawa 1 >