< 2 Sama’ila 1 >

1 Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
Or il arriva qu'après que Saül fut mort, David étant revenu de la défaite des Hamalécites, demeura à Tsiklag deux jours.
2 A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
Et au troisième jour, voici un homme qui revenait du camp de Saül, ayant ses vêtements déchirés, et de la terre sur sa tête, lequel étant venu à David, se jeta en terre, et se prosterna.
3 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
Et David lui dit: D'où viens-tu? et il lui répondit: Je me suis échappé du camp d'Israël.
4 Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
David lui dit: Qu'est-il arrivé? Je te prie, raconte-le moi. Il répondit: Le peuple s'est enfui de la bataille, et il y en a eu beaucoup du peuple qui sont tombés morts; Saül aussi et Jonathan son fils sont morts.
5 Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
Et David dit à ce jeune garçon qui lui disait ces nouvelles: Comment sais-tu que Saül et Jonathan son fils soient morts?
6 Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
Et le jeune garçon qui lui disait ces nouvelles, lui répondit: Je me trouvai par hasard en la montagne de Guilboah, et voici Saül se tenait penché sur sa hallebarde, car voici, un chariot et quelques Chefs de gens de cheval le poursuivaient.
7 Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
Et regardant derrière soi, il me vit, et m'appela; et je lui répondis: Me voici.
8 “Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
Et il me dit: Qui es-tu? et je lui répondis: Je suis Hamalécite.
9 “Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
Et il me dit: Tiens-toi ferme sur moi, je te prie, et me tue; car je suis dans une grande angoisse, et ma vie est encore toute en moi.
10 “Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
Je me suis donc tenu ferme sur lui, et je l'ai fait mourir; car je savais bien qu'il ne vivrait pas après s'être ainsi jeté sur sa hallebarde; et j'ai pris la couronne qu'il avait sur sa tête, et le bracelet qu'il avait en son bras, et je les ai apportés ici à mon Seigneur.
11 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
Alors David prit ses vêtements, et les déchira; et tous les hommes qui étaient avec lui en firent de même.
12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
Ils menèrent deuil, ils pleurèrent, et ils jeûnèrent jusqu'au soir, à cause de Saül et de Jonathan son fils, et à cause du peuple de l'Eternel, et de la maison d'Israël, parce qu'ils étaient tombés par l'épée.
13 Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
Mais David dit au jeune garçon qui lui avait dit ces nouvelles: D'où es-tu? Et il répondit: Je suis fils d'un étranger Hamalécite.
14 Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
Et David lui dit: Comment n'as-tu pas craint d'avancer ta main pour tuer l'Oint de l'Eternel?
15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
Alors David appela l'un de ses gens, et lui dit: Approche-toi, et te jette sur lui; lequel le frappa, et il mourut.
16 Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
Car David lui avait dit: Ton sang soit sur ta tête, puisque ta bouche a porté témoignage contre toi, en disant: J'ai fait mourir l'Oint de l'Eternel.
17 Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
Alors David fit sur Saül, et sur Jonathan son fils, cette complainte,
18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
[Laquelle] il proféra pour enseigner aux enfants de Juda [à tirer de] l'arc; voici elle est écrite au Livre de Jasar.
19 “Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
Ô noblesse d'Israël! ceux qui ont été tués sont sur tes hauts lieux. Comment sont tombés les hommes forts?
20 “Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
Ne l'allez point dire dans Gath, et n'en portez point les nouvelles dans les places d'Askélon; de peur que les filles des Philistins ne s'en réjouissent, de peur que les filles des incirconcis n'en tressaillent de joie.
21 “Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
Montagne de Guilboah, que la rosée et la pluie [ne tombent point] sur vous, ni sur les champs qui y sont haut élevés; parce que c'est là qu'a été jeté le bouclier des forts, et le bouclier de Saül, [comme s'il] n'eût point été oint d'huile.
22 “Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
L'arc de Jonathan ne revenait [jamais sans] le sang des morts, et sans la graisse des forts; et l'épée de Saül ne retournait [jamais] sans effet.
23 Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
Saül et Jonathan, aimables et agréables en leur vie, n'ont point été séparés dans leur mort; ils étaient plus légers que les aigles, ils étaient plus forts que des lions.
24 “Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
Filles d'Israël, pleurez sur Saül, qui faisait que vous étiez vêtues d'écarlate, que vous [viviez] dans les délices, [et] que vous portiez des ornements d'or sur vos vêtements.
25 “Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
Comment les forts sont-ils tombés au milieu de la bataille! [comment] Jonathan a-t-il été tué sur ces hauts lieux!
26 Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
Jonathan mon frère! Je suis dans l'angoisse pour l'amour de toi; tu faisais tout mon plaisir; l'amour que j'avais pour toi était plus grand que celui qu'on a pour les femmes.
27 “Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”
Comment sont tombés tes forts, et [comment] sont péris les instruments de guerre!

< 2 Sama’ila 1 >