< 2 Sama’ila 1 >

1 Bayan mutuwar Shawulu, Dawuda ya dawo daga karkashe Amalekawa. Sai ya zauna a Ziklag kwana biyu.
Et il arriva, après la mort de Saül, quand David fut revenu d’avoir frappé Amalek, que David habita deux jours à Tsiklag.
2 A rana ta uku sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Shawulu da yagaggen riga da ƙura a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi a ƙasa don yă nuna bangirma.
Et, le troisième jour, voici, un homme vint du camp, d’auprès de Saül, ses vêtements déchirés et de la terre sur sa tête; et aussitôt qu’il arriva auprès de David, il tomba contre terre et se prosterna.
3 Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Daga ina ka fito?” Ya amsa ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra’ila.”
Et David lui dit: D’où viens-tu? Et il lui dit: Je me suis échappé du camp d’Israël.
4 Dawuda ya ce, “Gaya mini, me ya faru?” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga yaƙi, aka kuma karkashe yawancin mutane. Shawulu da ɗansa Yonatan ma sun mutu.”
Et David lui dit: Que s’est-il passé? raconte-le-moi, je te prie. Et il dit que le peuple s’était enfui de la bataille, et que beaucoup d’entre le peuple étaient tombés et étaient morts, et que Saül aussi et Jonathan, son fils, étaient morts.
5 Sai Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Yaya ka san cewa Shawulu da ɗansa Yonatan sun mutu?”
Et David dit au jeune homme qui lui racontait [ces choses]: Comment sais-tu que Saül et Jonathan, son fils, sont morts?
6 Saurayin ya ce, “Ina kan dutsen Gilbowa a lokacin sai na ga Shawulu jingine a māshinsa. Kekunan yaƙi da mahayansu suna matsowa kusa da shi.
Et le jeune homme qui lui rapportait [ces choses] dit: Je passais par aventure sur la montagne de Guilboa; et voici, Saül s’appuyait sur sa lance, et voici, les chars et les gens de cheval le serraient de près.
7 Da ya juya ya gan ni sai ya kira ni, na kuwa ce masa, ‘Ga ni?’
Et il se tourna en arrière et me vit, et m’appela; et je dis: Me voici.
8 “Ya tambaye ni ya ce, ‘Wane ne kai?’ “Na ce, ‘Ni mutumin Amalek ne.’
Et il me dit: Qui es-tu? Et je lui dis: Je suis Amalékite.
9 “Sai ya ce mini, ‘Matso kusa ka kashe ni! Ina cikin azabar mutuwa, sai dai har yanzu ina da rai.’
Et il me dit: Tiens-toi, je te prie, sur moi, et tue-moi, car l’angoisse m’a saisi, parce que ma vie est encore toute en moi.
10 “Saboda haka na matso kusa da shi na kashe shi, domin na san cewa ba zai yi rai ba, da yake ya riga ya fāɗi. Sai na cire rawanin da yake kansa, na kuma cire warwaron hannunsa, na kuwa kawo maka su duka, ranka yă daɗe!”
Alors je me suis tenu sur lui, et je l’ai mis à mort; car je savais qu’il ne vivrait pas après sa chute; et j’ai pris la couronne qui était sur sa tête et le bracelet qui était à son bras, et je les ai apportés ici à mon seigneur.
11 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka yayyage rigunarsu.
Alors David saisit ses vêtements et les déchira; et tous les hommes qui étaient avec lui [firent] de même;
12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har yamma saboda Shawulu da ɗansa Yonatan, da saboda sojojin Ubangiji, da kuma gidan Isra’ila, gama an karkashe su a yaƙi.
et ils menèrent deuil, et pleurèrent, et jeûnèrent jusqu’au soir sur Saül et sur Jonathan, son fils, et sur le peuple de l’Éternel, et sur la maison d’Israël, parce qu’ils étaient tombés par l’épée.
13 Dawuda ya ce wa saurayin da ya kawo labarin, “Daga ina ka fito?” Ya ce, “Ni ɗan wani baƙo ne, mutumin Amalek.”
Et David dit au jeune homme qui lui avait rapporté [ces choses]: D’où es-tu? Et il dit: Je suis fils d’un homme étranger, d’un Amalékite.
14 Dawuda ya ce masa, “Yaya ba ka ji tsoro ɗaga hannu ka hallaka shafaffe na Ubangiji ba?”
Et David lui dit: Comment n’as-tu pas craint d’étendre ta main pour tuer l’oint de l’Éternel?
15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin mutanensa ya ce, “Je ka kashe shi!” Haka kuwa ya buge shi, ya kuwa mutu.
Alors David appela un des jeunes hommes et [lui] dit: Approche [et] jette-toi sur lui! Et il le frappa, et il mourut.
16 Gama Dawuda ya riga ya ce masa, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe shafaffe na Ubangiji.’”
Et David lui dit: Ton sang soit sur ta tête, car ta bouche a témoigné contre toi, disant: J’ai mis à mort l’oint de l’Éternel.
17 Dawuda ya rera wannan makoki saboda Shawulu da ɗansa Yonatan.
Et David prononça sur Saül et sur Jonathan, son fils, cette complainte;
18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuda wannan waƙa mai suna Makokin Baka (tana a rubuce a Littafin Yashar),
et il dit d’enseigner aux fils de Juda [le chant de] l’Arc; voici, il est écrit au livre de Jashar:
19 “Ya Isra’ila, an kashe darajarki a kan tuddanki. Ga shi, jarumawa sun fāɗi!
Ton ornement, ô Israël, est tué sur tes hauts lieux. Comment les hommes forts sont-ils tombés!
20 “Kada a faɗe shi a Gat, kada a yi shelarsa a titunan Ashkelon, don kada’yan matan Filistiyawa su yi murna don kada’yan matan marasa kaciya su yi farin ciki.
Ne le racontez pas dans Gath, n’en portez pas la nouvelle dans les rues d’Askalon; de peur que les filles des Philistins ne se réjouissent, de peur que les filles des incirconcis ne tressaillent de joie.
21 “Ya duwatsun Gilbowa, kada a sāke yin ruwa ko raɓa a kanku, balle gonakin da suke ba da hatsin hadaya su ƙara bayarwa. Gama a can ne garkuwoyin manyan sojoji suka kwanta, suka kwanta a wulaƙance. Garkuwar Shawulu kuwa, ba za a ƙara shafa mata mai ba.
Montagnes de Guilboa, qu’il n’y ait pas de rosée, pas de pluie sur vous, ni des champs d’offrandes; car là fut jeté comme une chose souillée le bouclier des hommes forts, le bouclier de Saül, [comme s’il n’avait] pas été oint d’huile.
22 “Daga jinin waɗanda aka kashe, daga tsokar naman jarumi, bakan Yonatan bai juye baya ba, takobin Shawulu bai komo ba tare da gamsuwa ba.
L’arc de Jonathan ne se retirait pas du sang des tués [et] de la graisse des hommes forts; et l’épée de Saül ne retournait pas à vide.
23 Shawulu da Yonatan, a raye ƙaunatattu ne da kuma bansha’awa, a mace kuma ba su rabu ba. Sun fi gaggafa sauri, sun fi zaki ƙarfi.
Saül et Jonathan, aimés et agréables dans leur vie, n’ont pas été séparés dans leur mort. Ils étaient plus rapides que les aigles, plus forts que les lions.
24 “Ya ku’yan matan Isra’ila, ku yi kuka saboda Shawulu, wanda ya suturta ku da jajjayen kayan ado, wanda ya yi wa rigunarku ado da zinariya.
Filles d’Israël, pleurez sur Saül, qui vous revêtait d’écarlate, magnifiquement, qui a couvert vos vêtements d’ornements d’or.
25 “Jarumawa sun fāɗi a yaƙi! Ga Yonatan matacce a tuddanku.
Comment les hommes forts sont-ils tombés au milieu de la bataille! Comment Jonathan a-t-il été tué sur tes hauts lieux!
26 Na yi baƙin ciki saboda kai, Yonatan ɗan’uwana; ƙaunatacce kake a gare ni. Ƙaunarka a gare ni abar al’ajabi ce, abar al’ajabi fiye da ta mace.
Je suis dans l’angoisse à cause de toi, Jonathan, mon frère! Tu étais pour moi plein de charmes; ton amour pour moi était merveilleux, plus [grand] que l’amour des femmes.
27 “Jarumawa sun fāɗi! Makaman yaƙi sun hallaka!”
Comment sont tombés les hommes forts, et ont péris les instruments de guerre!

< 2 Sama’ila 1 >