< 2 Sama’ila 9 >
1 Wata rana Dawuda ya yi tambaya ya ce, “Akwai wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu wanda zan nuna masa alheri saboda Yonatan?”
Un Dāvids sacīja: vai vēl ir kāds, kas atlicies no Saula nama, ka es tam žēlastību parādu Jonatāna dēļ?
2 To, akwai wani bawa na gidan Shawulu mai suna Ziba. Sai aka kira shi yă bayyana a gaban Dawuda, sarki ya ce masa, “Kai ne Ziba?” Sai ya ce, “I, ni ne, ranka yă daɗe.”
Un Saula namam bija kalps, Cībus vārdā, un tas tapa aicināts Dāvida priekšā. Un ķēniņš uz to sacīja: vai tu esi Cībus? Un viņš sacīja: esmu, tavs kalps.
3 Sa’an nan sarki ya yi tambaya ya ce, “Babu wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu don in nuna masa alherin Allah?” Ziba ya ce wa sarki, “Har yanzu akwai ɗan Yonatan da ya rage, sai dai shi gurgu ne a dukan ƙafafu.”
Un ķēniņš sacīja: vai vēl kāds nav no Saula nama, ka es Dieva žēlastību tam parādu? Un Cībus sacīja uz ķēniņu: Vēl ir viens Jonatāna dēls, tizls uz abām kājām.
4 Sarki ya ce, “Ina yake?” Ziba ya ce, “Yana a gidan Makir ɗan Ammiyel a Lo Debar.”
Un ķēniņš uz to sacīja: kur tas ir? Un Cībus sacīja uz ķēniņu: redzi, viņš ir Mahira, Amiēļa dēla, namā, Lodabarā.
5 Saboda haka Sarki Dawuda ya umarta aka kawo shi daga gidan Makir ɗan Ammiyel, daga Lo Debar.
Tad ķēniņš Dāvids nosūtīja un to ņēma no Mahira, Amiēļa dēla, nama, no Lodabaras.
6 Sa’ad da Mefiboshet ɗan Yonatan, ɗan Shawulu, ya zo wurin Dawuda, sai ya rusuna har ƙasa ya yi gaisuwar bangirma. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Shi kuwa ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, ga ni, bawanka.”
Kad nu Mefibošets, Jonatāna dēls, Saula dēla dēls, pie Dāvida nāca tad viņš metās uz savu vaigu un klanījās. Un Dāvids sacīja: Mefibošet! Un viņš sacīja: redzi, še tavs kalps.
7 Dawuda ya ce, “Kada ka ji tsoro, gama tabbatacce zan nuna maka alheri saboda mahaifinka Yonatan. Zan mayar maka da dukan ƙasar da take ta kakanka Shawulu, kullum kuma za ka ci a teburina.”
Un Dāvids uz to sacīja: nebīsties, es tiešām tev parādīšu žēlastību tava tēva Jonatāna dēļ, un tev atdošu visus tava tēva Saula tīrumus, un tev būs vienmēr maizi ēst pie mana galda.
8 Mefiboshet ya rusuna ya ce, “Ni ne wa har da za ka kula da ni? Ai! Ni bawanka ne da bai ma fi mataccen kare daraja ba.”
Un tas paklanījās un sacīja: kas tavs kalps tāds ir, ka tu uzlūko nomirušu suni, kāds es esmu?
9 Sai sarki ya kira Ziba bawan Shawulu, ya ce masa, “Na ba wa jikan maigidanka kome da yake na Shawulu da iyalinsa
Tad ķēniņš aicināja Cību, Saula kalpu, un uz to sacīja: visu, kas Saulam un viņa namam piederēja, to es esmu devis tava kunga dēlam.
10 Kai da’ya’yanka maza da bayinka za ku riƙa yin masa noma, ku kuma kawo hatsin, don jikan maigidanka yă sami abinci. Mefiboshet kuma, jikan maigidanka, zai riƙa ci a teburina.” (Ziba kuwa yana da’ya’ya maza goma sha biyar da kuma bayi ashirin.)
Tāpēc strādā tu viņam to zemi, tu ar saviem dēliem un ar saviem kalpiem, un savāc, ka tava kunga dēlam ir maizes ko ēst, un Mefibošets, tava kunga dēls, lai vienmēr ēd maizi pie mana galda. Bet Cībum bija piecpadsmit dēli un divdesmit kalpi.
11 Sai Ziba ya ce wa sarki, “Bawanka zai aikata dukan abin da ranka yă daɗe sarki, ya umarce shi.” Saboda haka Mefiboshet ya riƙa ci a teburin Dawuda kamar sauran’ya’yan sarki.
Un Cībus sacīja uz ķēniņu: visu, ko mans kungs, tas ķēniņš, savam kalpam pavēl, to tavs kalps darīs. Un Mefibošets lai ēd pie mana galda tāpat, kā viens no ķēniņa bērniem.
12 Mefiboshet yana da wani ƙaramin ɗa sunansa Mika, dukan iyalin gidan Ziba kuwa bayin Mefiboshet ne.
Un Mefibošetam bija mazs dēls, vārdā Miha, un visi, kas Cībus namā dzīvoja, tie Mefibošetam bija par kalpiem.
13 Mefiboshet ya zauna a Urushalima, gama kullum yana ci a teburin sarki, shi kuwa gurgu ne a dukan ƙafafu.
Un Mefibošets dzīvoja Jeruzālemē, tāpēc ka viņš vienmēr ēda pie ķēniņa galda. Un viņš bija tizls uz abām kājām.