< 2 Sama’ila 9 >
1 Wata rana Dawuda ya yi tambaya ya ce, “Akwai wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu wanda zan nuna masa alheri saboda Yonatan?”
And David said, Is there yet any one that is left of the house of Saul, that I may show him kindness for the sake of Jonathan?
2 To, akwai wani bawa na gidan Shawulu mai suna Ziba. Sai aka kira shi yă bayyana a gaban Dawuda, sarki ya ce masa, “Kai ne Ziba?” Sai ya ce, “I, ni ne, ranka yă daɗe.”
And the house of Saul had a servant whose name was Ziba; and they called him unto David; and the king said unto him, Art thou Ziba? And be said, Thy servant [is it].
3 Sa’an nan sarki ya yi tambaya ya ce, “Babu wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu don in nuna masa alherin Allah?” Ziba ya ce wa sarki, “Har yanzu akwai ɗan Yonatan da ya rage, sai dai shi gurgu ne a dukan ƙafafu.”
And the king said, Is there no one left any more of the house of Saul, that I may show him the kindness of God! And Ziba said unto the king, There is yet a son of Jonathan, lame on both feet.
4 Sarki ya ce, “Ina yake?” Ziba ya ce, “Yana a gidan Makir ɗan Ammiyel a Lo Debar.”
And the king said unto him, Where is he? And Ziba said unto the king, Behold, he is in the house of Machir, the son of 'Ammiel, in Lo-debar.
5 Saboda haka Sarki Dawuda ya umarta aka kawo shi daga gidan Makir ɗan Ammiyel, daga Lo Debar.
And king David sent, and had him taken out of the house of Machir, the son of 'Ammiel, from Lo-debar.
6 Sa’ad da Mefiboshet ɗan Yonatan, ɗan Shawulu, ya zo wurin Dawuda, sai ya rusuna har ƙasa ya yi gaisuwar bangirma. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Shi kuwa ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, ga ni, bawanka.”
And Mephibosheth, the son of Jonathan, the son of Saul, came unto David, and he fell on his face, and bowed himself. And David said, Mephibosheth; And he answered, Here is thy servant!
7 Dawuda ya ce, “Kada ka ji tsoro, gama tabbatacce zan nuna maka alheri saboda mahaifinka Yonatan. Zan mayar maka da dukan ƙasar da take ta kakanka Shawulu, kullum kuma za ka ci a teburina.”
And David said unto him, Fear not; for I will surely show thee kindness for the sake of Jonathan thy father, and I will restore unto thee all the land of Saul thy father; and thou shalt eat bread at my table continually.
8 Mefiboshet ya rusuna ya ce, “Ni ne wa har da za ka kula da ni? Ai! Ni bawanka ne da bai ma fi mataccen kare daraja ba.”
And he bowed himself, and said, What is thy servant, that thou shouldst turn thy regard unto such a dead dog as I am?
9 Sai sarki ya kira Ziba bawan Shawulu, ya ce masa, “Na ba wa jikan maigidanka kome da yake na Shawulu da iyalinsa
Then called the king for Ziba, Saul's servant, and said unto him, all that hath pertained to Saul and to all his house have I given unto thy master's son.
10 Kai da’ya’yanka maza da bayinka za ku riƙa yin masa noma, ku kuma kawo hatsin, don jikan maigidanka yă sami abinci. Mefiboshet kuma, jikan maigidanka, zai riƙa ci a teburina.” (Ziba kuwa yana da’ya’ya maza goma sha biyar da kuma bayi ashirin.)
And thou shalt till for him the land, thou, and thy sons, and thy servants, and thou shalt bring in [the product], that thy master's son may have bread which he can eat; but Mephibosheth thy master's son shall eat continually bread at my table. Now Ziba had fifteen sons and twenty servants.
11 Sai Ziba ya ce wa sarki, “Bawanka zai aikata dukan abin da ranka yă daɗe sarki, ya umarce shi.” Saboda haka Mefiboshet ya riƙa ci a teburin Dawuda kamar sauran’ya’yan sarki.
And Ziba said unto the king, In accordance with all that my Lord the king may command his servant, so will thy servant do. And Mephibosheth [said the king] shall eat at my table, as one of the king's sons.
12 Mefiboshet yana da wani ƙaramin ɗa sunansa Mika, dukan iyalin gidan Ziba kuwa bayin Mefiboshet ne.
And Mephibosheth had a young son, whose name was Micha. And all that dwelt in the house of Ziba were servants unto Mephibosheth.
13 Mefiboshet ya zauna a Urushalima, gama kullum yana ci a teburin sarki, shi kuwa gurgu ne a dukan ƙafafu.
And Mephibosheth dwelt in Jerusalem; for he ate continually at the king's table; and he was lame on both his feet.