< 2 Sama’ila 9 >

1 Wata rana Dawuda ya yi tambaya ya ce, “Akwai wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu wanda zan nuna masa alheri saboda Yonatan?”
And David said, Is there yet any that is left of the house of Saul, that I may show him kindness for Jonathan’s sake?
2 To, akwai wani bawa na gidan Shawulu mai suna Ziba. Sai aka kira shi yă bayyana a gaban Dawuda, sarki ya ce masa, “Kai ne Ziba?” Sai ya ce, “I, ni ne, ranka yă daɗe.”
And there was of the house of Saul a servant whose name was Ziba. And when they had called him to David, the king said to him, Are you Ziba? And he said, Your servant is he.
3 Sa’an nan sarki ya yi tambaya ya ce, “Babu wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu don in nuna masa alherin Allah?” Ziba ya ce wa sarki, “Har yanzu akwai ɗan Yonatan da ya rage, sai dai shi gurgu ne a dukan ƙafafu.”
And the king said, Is there not yet any of the house of Saul, that I may show the kindness of God to him? And Ziba said to the king, Jonathan has yet a son, which is lame on his feet.
4 Sarki ya ce, “Ina yake?” Ziba ya ce, “Yana a gidan Makir ɗan Ammiyel a Lo Debar.”
And the king said to him, Where is he? And Ziba said to the king, Behold, he is in the house of Machir, the son of Ammiel, in Lodebar.
5 Saboda haka Sarki Dawuda ya umarta aka kawo shi daga gidan Makir ɗan Ammiyel, daga Lo Debar.
Then king David sent, and fetched him out of the house of Machir, the son of Ammiel, from Lodebar.
6 Sa’ad da Mefiboshet ɗan Yonatan, ɗan Shawulu, ya zo wurin Dawuda, sai ya rusuna har ƙasa ya yi gaisuwar bangirma. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Shi kuwa ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, ga ni, bawanka.”
Now when Mephibosheth, the son of Jonathan, the son of Saul, was come to David, he fell on his face, and did reverence. And David said, Mephibosheth. And he answered, Behold your servant!
7 Dawuda ya ce, “Kada ka ji tsoro, gama tabbatacce zan nuna maka alheri saboda mahaifinka Yonatan. Zan mayar maka da dukan ƙasar da take ta kakanka Shawulu, kullum kuma za ka ci a teburina.”
And David said to him, Fear not: for I will surely show you kindness for Jonathan your father’s sake, and will restore you all the land of Saul your father; and you shall eat bread at my table continually.
8 Mefiboshet ya rusuna ya ce, “Ni ne wa har da za ka kula da ni? Ai! Ni bawanka ne da bai ma fi mataccen kare daraja ba.”
And he bowed himself, and said, What is your servant, that you should look on such a dead dog as I am?
9 Sai sarki ya kira Ziba bawan Shawulu, ya ce masa, “Na ba wa jikan maigidanka kome da yake na Shawulu da iyalinsa
Then the king called to Ziba, Saul’s servant, and said to him, I have given to your master’s son all that pertained to Saul and to all his house.
10 Kai da’ya’yanka maza da bayinka za ku riƙa yin masa noma, ku kuma kawo hatsin, don jikan maigidanka yă sami abinci. Mefiboshet kuma, jikan maigidanka, zai riƙa ci a teburina.” (Ziba kuwa yana da’ya’ya maza goma sha biyar da kuma bayi ashirin.)
You therefore, and your sons, and your servants, shall till the land for him, and you shall bring in the fruits, that your master’s son may have food to eat: but Mephibosheth your master’s son shall eat bread always at my table. Now Ziba had fifteen sons and twenty servants.
11 Sai Ziba ya ce wa sarki, “Bawanka zai aikata dukan abin da ranka yă daɗe sarki, ya umarce shi.” Saboda haka Mefiboshet ya riƙa ci a teburin Dawuda kamar sauran’ya’yan sarki.
Then said Ziba to the king, According to all that my lord the king has commanded his servant, so shall your servant do. As for Mephibosheth, said the king, he shall eat at my table, as one of the king’s sons.
12 Mefiboshet yana da wani ƙaramin ɗa sunansa Mika, dukan iyalin gidan Ziba kuwa bayin Mefiboshet ne.
And Mephibosheth had a young son, whose name was Micha. And all that dwelled in the house of Ziba were servants to Mephibosheth.
13 Mefiboshet ya zauna a Urushalima, gama kullum yana ci a teburin sarki, shi kuwa gurgu ne a dukan ƙafafu.
So Mephibosheth dwelled in Jerusalem: for he did eat continually at the king’s table; and was lame on both his feet.

< 2 Sama’ila 9 >