< 2 Sama’ila 9 >

1 Wata rana Dawuda ya yi tambaya ya ce, “Akwai wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu wanda zan nuna masa alheri saboda Yonatan?”
David sagde: "Er der endnu nogen tilbage af Sauls Hus? Så vil jeg vise Godhed imod ham for Jonatans Skyld!"
2 To, akwai wani bawa na gidan Shawulu mai suna Ziba. Sai aka kira shi yă bayyana a gaban Dawuda, sarki ya ce masa, “Kai ne Ziba?” Sai ya ce, “I, ni ne, ranka yă daɗe.”
Nu var der i Sauls Hus en Træl ved Navn Ziba; han blev kaldt op til David, og Kongen sagde til ham:"Er du Ziba?" Han svarede: "Ja, det er din Træl!"
3 Sa’an nan sarki ya yi tambaya ya ce, “Babu wani har yanzu da ya rage a gidan Shawulu don in nuna masa alherin Allah?” Ziba ya ce wa sarki, “Har yanzu akwai ɗan Yonatan da ya rage, sai dai shi gurgu ne a dukan ƙafafu.”
Da sagde Kongen: "Er der ingen tilbage af Sauls Hus? Så vil jeg vise Guds Godhed imod ham." Ziba svarede Kongen: "Der lever endnu en Søn af Jonatan; han er lam i Fødderne."
4 Sarki ya ce, “Ina yake?” Ziba ya ce, “Yana a gidan Makir ɗan Ammiyel a Lo Debar.”
Da spurgte Kongen: "Hvor er han?" Og Ziba svarede Kongen: "Han er i Makirs, Ammiels Søns, Hus i Lodebar."
5 Saboda haka Sarki Dawuda ya umarta aka kawo shi daga gidan Makir ɗan Ammiyel, daga Lo Debar.
Så lod Kong David ham hente i Makirs, Ammiels Søns, Hus i Lodebar.
6 Sa’ad da Mefiboshet ɗan Yonatan, ɗan Shawulu, ya zo wurin Dawuda, sai ya rusuna har ƙasa ya yi gaisuwar bangirma. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Shi kuwa ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, ga ni, bawanka.”
Da Mefibosjet, Sauls Søn Jonatans Søn, kom ind til David, faldt han på sit Ansigt og bøjede sig. David sagde: "Mefibosjet!" Han svarede: "Ja, her er din Træl!"
7 Dawuda ya ce, “Kada ka ji tsoro, gama tabbatacce zan nuna maka alheri saboda mahaifinka Yonatan. Zan mayar maka da dukan ƙasar da take ta kakanka Shawulu, kullum kuma za ka ci a teburina.”
David sagde til ham: "Frygt ikke! Jeg vil vise dig Godhed for din Fader Jonatans Skyld og give dig hele din Fader Sauls Jordegods tilbage; og du skal altid spise ved mit Bord."
8 Mefiboshet ya rusuna ya ce, “Ni ne wa har da za ka kula da ni? Ai! Ni bawanka ne da bai ma fi mataccen kare daraja ba.”
Da bøjede han sig og sagde: "Hvad er din Træl, siden du tager Hensyn til en død Hund som mig?"
9 Sai sarki ya kira Ziba bawan Shawulu, ya ce masa, “Na ba wa jikan maigidanka kome da yake na Shawulu da iyalinsa
Derpå lod Kongen Sauls Tjener Ziba kalde og sagde til ham: "Alt, hvad der tilhørte Saul og hele hans Hus, har jeg givet din Herres Søn;
10 Kai da’ya’yanka maza da bayinka za ku riƙa yin masa noma, ku kuma kawo hatsin, don jikan maigidanka yă sami abinci. Mefiboshet kuma, jikan maigidanka, zai riƙa ci a teburina.” (Ziba kuwa yana da’ya’ya maza goma sha biyar da kuma bayi ashirin.)
men du tillige med dine Sønner og Trælle skal dyrke Jorden og indhøste Afgrøden, for at din Herres Hus kan have sit Underhold deraf; men din Herres Søn Mefibosjet skal altid spise ved mit Bord." Ziba havde femten Sønner og tyve Trælle.
11 Sai Ziba ya ce wa sarki, “Bawanka zai aikata dukan abin da ranka yă daɗe sarki, ya umarce shi.” Saboda haka Mefiboshet ya riƙa ci a teburin Dawuda kamar sauran’ya’yan sarki.
Da sagde Ziba til Kongen: "Din Træl vil gøre, ganske som min Herre Kongen byder!" Mefibosjet spiste så ved Davids Bord, som var han en af Kongens Sønner.
12 Mefiboshet yana da wani ƙaramin ɗa sunansa Mika, dukan iyalin gidan Ziba kuwa bayin Mefiboshet ne.
Mefibosjet havde en lille Søn ved Navn Mika. Hele Zibas Husstand var Mefibosjets Trælle.
13 Mefiboshet ya zauna a Urushalima, gama kullum yana ci a teburin sarki, shi kuwa gurgu ne a dukan ƙafafu.
Og Mefibosjet boede i Jerusalem, thi han spiste altid ved Kongens Bord. Og han var lam i begge Fødder.

< 2 Sama’ila 9 >