< 2 Sama’ila 8 >
1 Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
Och det begaf sig derefter, att David slog de Philisteer, och förnedrade dem, och tog träldomsbetslet utu de Philisteers hand.
2 Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
Han slog ock de Moabiter så till jordena, att han två delar drap, och en del lät lefvandes blifva. Alltså vordo de Moabiter David underdånige, så att de förde skänker till honom.
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
David slog ock HadadEser, Rehobs son, Konungen i Zoba, då han drog ut till att hemta sin magt igen, vid den älfven Phrath.
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
Och David fångade af dem tusende och sjuhundrad resenärar, och tjugutusend fotfolk; och hasade alla vagnhästar, och behöll qvar hundrade vagnar.
5 Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
Så kommo de Syrer af Damascon, till att hjelpa HadadEser, Konungen i Zoba; och David slog de Syrer, tu och tjugu tusend män;
6 Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Och lade folk till Damascon i Syria. Alltså vardt Syria David underdånig, så att de förde skänker till honom; ty Herren halp David, ehvart han drog.
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
Och David tog de gyldene sköldar, som HadadEsers tjenare tillhört hade, och förde dem till Jerusalem.
8 Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
Men ifrå Bethah, och Berothai, HadadEsers städer, tog Konung David ganska mycken koppar.
9 Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
Då Thoi, Konungen i Hemath, hörde att David hade slagit alla HadadEsers magt,
10 sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
Sände han Joram sin son till David, till att helsa honom vänliga, och välsigna honom, att han hade stridt med HadadEser, och slagit honom; ty Thoi hade örlig med HadadEser, och han hade med sig silfver, och gyldene, och koppartyg;
11 Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
Hvilka Konung David ock helgade Herranom, samt med det silfver och guld, som han helgade af allom Hedningom, dem han under sig tvingade,
12 wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
Af Syria, af Moab, af Ammons barn, af de Philisteer, af Amalek, af HadadEsers rof, Rehobs sons, Konungens i Zoba.
13 Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
Och gjorde David sig ett namn, då han igenkom och slog de Syrer i saltdalenom, adertontusend.
14 Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Och han lade folk i hela Edomea; och hela Edom var David undergifven; ty Herren halp David, ehvart han drog.
15 Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
Alltså vardt David Konung öfver hela Israel; och han skaffade rätt och rättviso allo folkena.
16 Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
Joab, ZeruJa son, var öfver hären; men Josaphat, Ahiluds son, var canceller.
17 Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
Zadok, Ahitobs son, och Ahimelech, AbJathars son, voro Prester; Seraja var skrifvare;
18 Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.
Benaja, Jojada son, var öfver Crethi och Plethi; och Davids söner voro Prester.