< 2 Sama’ila 8 >

1 Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
Depois disso, David bateu nos filisteus e os subjugou; e David tirou o freio da cidade mãe da mão dos filisteus.
2 Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
Ele derrotou Moab e os mediu com a linha, fazendo-os deitar no chão; e mediu duas linhas até a morte, e uma linha completa para se manterem vivos. Os moabitas se tornaram servos de David, e trouxeram tributo.
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
David também atingiu Hadadezer, filho de Rehob, rei de Zobah, quando ele foi recuperar seu domínio no rio.
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
David tirou dele mil setecentos cavaleiros e vinte mil homens de pé. Davi empurrou os cavalos das carruagens, mas reservou o suficiente deles para cem carruagens.
5 Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
Quando os sírios de Damasco vieram para ajudar Hadadezer, rei de Zobah, David atingiu vinte e dois mil homens dos sírios.
6 Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Então Davi colocou guarnições na Síria de Damasco; e os sírios se tornaram servos de Davi, e trouxeram tributo. Yahweh deu vitória a Davi onde quer que ele fosse.
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
David pegou os escudos de ouro que estavam sobre os servos de Hadadezer, e os trouxe para Jerusalém.
8 Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
De Betah e de Berothai, cidades de Hadadezer, o rei Davi tomou uma grande quantidade de bronze.
9 Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
Quando Toi, rei de Hamath, soube que David havia atingido todo o exército de Hadadezer,
10 sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
então Toi enviou seu filho Jorão ao rei David para saudá-lo e abençoá-lo, pois ele havia lutado contra Hadadezer e batido nele; pois Hadadezer tinha guerras com Toi. Jorão trouxe com ele vasos de prata, vasos de ouro e vasos de bronze.
11 Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
O rei David também os dedicou a Iavé, com a prata e o ouro que ele dedicou a todas as nações que ele subjugou -
12 wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
da Síria, dos Moab, dos filhos de Amon, dos filisteus, de Amalek, e do saque de Hadadezer, filho de Rehob, rei de Zobah.
13 Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
David ganhou uma reputação quando retornou do ataque a dezoito mil homens dos sírios no Vale do Sal.
14 Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Ele colocou guarnições em Edom. Em todos os Edom, ele colocou guarnições, e todos os Edomitas se tornaram servos de Davi. Yahweh deu vitória a David para onde quer que ele fosse.
15 Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
David reinou sobre todo Israel; e David executou justiça e retidão para todo o seu povo.
16 Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
Joabe, filho de Zeruia, estava sobre o exército, Jeosafá, filho de Ailude, era registrador,
17 Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
Zadoque, filho de Aitube, e Aimeleque, filho de Abiatar, eram sacerdotes, Seraías, escriba,
18 Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.
Benaías, filho de Jeoiada, estava sobre os queretitas e os peletitas; e os filhos de Davi eram ministros chefes.

< 2 Sama’ila 8 >