< 2 Sama’ila 8 >

1 Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
Or, il arriva après cela que [David battit les Philistins et les humilia; et David ôta le frein du tribut de la main des Philistins.
2 Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
Il battit aussi Moab et les mesura au cordeau, les faisant coucher par terre; or, il en mesura deux cordeaux, l’un pour les tuer, l’autre pour leur conserver la vie; et Moab fut assujetti à David lui payant tribut.
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
De plus, David battit Adarézer, fils de Rohob, roi de Soba, quand il partit pour dominer sur le fleuve d’Euphrate.
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
Et David, après lui avoir pris mille sept cents cavaliers et vingt mille hommes de pied, coupa les nerfs des jambes à tous les chevaux des chariots; mais il en laissa pour cent chariots.
5 Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
Vint aussi la Syrie de Damas, pour porter secours à Adarézer, roi de Soba; et David tua vingt-deux mille hommes de la Syrie.
6 Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Et David mit une garnison dans la Syrie de Damas; et la Syrie devint tributaire de David; et le Seigneur conserva David dans tous les lieux où il alla.
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
Et David enleva les armes d’or qu’avaient les serviteurs d’Adarézer, et les porta à Jérusalem.
8 Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
Et de Beté et de Béroth, villes d’Adarézer, le roi David enleva une très grande quantité d’airain.
9 Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
Or, Thoü, roi d’Emath, apprit que David avait battu toutes les forces d’Adarézer;
10 sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
Alors il envoya Joram son fils vers le roi David, pour le saluer, en le félicitant, et lui rendre grâce de ce qu’il avait vivement attaqué Adarézer, et l’avait battu; car Thoü était ennemi d’Adarézer; et dans la main de Joram étaient des vases d’or, des vases d’argent et des vases d’airain,
11 Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
Que le roi David consacra aussi au Seigneur, avec l’argent et l’or qu’il avait consacrés de toutes les nations qu’il avait soumises,
12 wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
De la Syrie, de Moab, des enfants d’Ammon, des Philistins, d’Amalec et des dépouilles d’Adarézer, fils de Rohob, roi de Soba.
13 Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
David se fit encore un nom, lorsque, la Syrie prise, il fut revenu dans la vallée des Salines, où il tailla en pièces dix-huit mille hommes.
14 Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Et il mit des gardes dans l’Idumée, et il établit une garnison; et toute l’Idumée devint assujettie à David; et le Seigneur conserva David dans tous les lieux où il alla.
15 Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
Ainsi David régna sur tout Israël; il rendait aussi des jugements et la justice à tout son peuple.
16 Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
Mais Joab, fils de Sarvia, commandait l’armée, et Josaphat, fils d’Ahilud, tenait les registres;
17 Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
Et Sadoc, fils d’Achitob, et Achimélech, fils d’Abiathar, étaient prêtres, et Saraïas, scribe;
18 Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.
Mais Banaïas, fils de Joïada, commandait les Céréthiens et les Phéléthiens; mais les fils de David étaient prêtres.

< 2 Sama’ila 8 >