< 2 Sama’ila 8 >

1 Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
Après cela il arriva que David battit les Philistins, et les abaissa, et David prit Methegamma de la main des Philistins.
2 Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
Il battit aussi les Moabites, et les mesura au cordeau, les faisant coucher par terre; et il en mesura deux cordeaux pour les faire mourir, et un plein cordeau pour leur sauver la vie; et [le pays] des Moabites fut à David sous cette condition, qu'ils lui seraient sujets et tributaires.
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
David battit aussi Hadadhézer fils de Réhob, Roi de Tsoba, comme il allait pour recouvrer ses limites sur le fleuve d'Euphrate.
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
Et David lui prit mille et sept cents hommes de cheval, et vingt mille hommes de pied, et coupa les jarrets [des chevaux] de tous les chariots, mais il en réserva cent chariots.
5 Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
Car les Syriens de Damas étaient venus pour donner du secours à Hadadhézer Roi de Tsoba; et David battit vingt-deux mille Syriens.
6 Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Puis David mit garnison en Syrie de Damas, et [le pays] de ces Syriens fut à David sous cette condition, qu'ils lui seraient sujets et tributaires; et l'Eternel gardait David partout où il allait.
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
Et David prit les boucliers d'or qui étaient aux serviteurs de Hadadhézer, et les apporta à Jérusalem.
8 Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
Le Roi David emporta aussi une grande quantité d'airain de Bétah, et de Bérothaï, villes de Hadadhézer.
9 Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
Or Tohi, Roi de Hamath, apprit que David avait défait toutes les forces de Hadadhézer.
10 sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
Et il envoya Joram son fils vers le Roi David, pour le saluer, et le féliciter de ce qu'il avait fait la guerre contre Hadadhézer, et de ce qu'il l'avait défait; car Hadadhézer était en guerre continuellement avec Tohi, et [Joram] apporta des vaisseaux d'argent, et des vaisseaux d'or, et des vaisseaux d'airain;
11 Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
Lesquels David consacra à l'Eternel avec l'argent et l'or qu'il avait [déjà] consacrés [du butin] de toutes les nations qu'il s'était assujetties;
12 wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
De Syrie, de Moab, des enfants de Hammon, des Philistins, de Hamalec, et du butin de Hadadhézer, fils de Réhob, Roi de Tsoba.
13 Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
David s'acquit aussi [une grande] réputation de ce qu'en retournant de la défaite des Syriens, [il tailla en pièces] dans la vallée du sel dix-huit mille Iduméens.
14 Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Et il mit garnison dans l'Idumée, il mit, dis-je, garnison dans toute l'Idumée; et tous les Iduméens furent assujettis à David; et l'Eternel gardait David partout où il allait.
15 Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
Ainsi David régna sur tout Israël, faisant droit et justice à tout son peuple.
16 Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
Et Joab fils de Tséruja avait la charge de l'armée; et Jéhosaphat fils d'Ahilud, était commis sur les registres.
17 Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
Et Tsadok fils d'Ahitub, et Ahimélec fils d'Abiathar étaient les Sacrificateurs, et Séraja était le Secrétaire.
18 Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.
Et Bénaja fils de Jéhojadah était sur les Kéréthiens et les Péléthiens; et les fils de David étaient les principaux Officiers.

< 2 Sama’ila 8 >