< 2 Sama’ila 8 >
1 Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
Et il arriva, après cela, que David frappa les Philistins et les subjugua; et David prit Métheg-Amma de la main des Philistins.
2 Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
Et il frappa Moab, et il les mesura au cordeau, les faisant coucher par terre, et il en mesura deux cordeaux pour les faire mourir, et un plein cordeau pour les laisser vivre; et les Moabites devinrent serviteurs de David: ils lui apportèrent des présents.
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
Et David frappa Hadadézer, fils de Rehob, roi de Tsoba, comme il allait pour rétablir sa puissance sur le fleuve [Euphrate].
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
Et David lui prit 1 700 cavaliers et 20 000 hommes de pied; et David coupa les jarrets [aux chevaux] de tous les chars, mais il réserva 100 attelages.
5 Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
Et les Syriens de Damas vinrent au secours d’Hadadézer, roi de Tsoba; et David frappa 22 000 hommes des Syriens.
6 Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Et David mit des garnisons dans la Syrie de Damas, et les Syriens devinrent serviteurs de David: ils lui apportèrent des présents. Et l’Éternel sauvait David partout où il allait.
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
Et David prit les boucliers d’or qui étaient aux serviteurs d’Hadadézer, et les apporta à Jérusalem.
8 Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
Et de Bétakh et de Bérothaï, villes d’Hadadézer, le roi David prit une grande quantité d’airain.
9 Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
Et Tohi, roi de Hamath, apprit que David avait frappé toutes les forces d’Hadadézer.
10 sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
Et Tohi envoya Joram, son fils, au roi David, pour le saluer et le féliciter de ce qu’il avait fait la guerre à Hadadézer et l’avait battu; car Hadadézer était continuellement en guerre avec Tohi; et [Joram] avait avec lui des vases d’argent, et des vases d’or, et des vases d’airain.
11 Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
Ceux-ci aussi, le roi David les consacra à l’Éternel, avec l’argent et l’or qu’il avait consacrés de toutes les nations qu’il avait soumises:
12 wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
de Syrie, et de Moab, et des fils d’Ammon, et des Philistins, et d’Amalek, et du butin d’Hadadézer, fils de Rehob, roi de Tsoba.
13 Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
Et David se fit un nom, en revenant d’avoir frappé les Syriens dans la vallée du Sel, [au nombre de] 18 000.
14 Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Et il mit des garnisons en Édom; il mit des garnisons dans tout Édom, et tout Édom fut asservi à David. Et l’Éternel sauvait David partout où il allait.
15 Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
Et David régna sur tout Israël; et David faisait droit et justice à tout son peuple.
16 Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
Et Joab, fils de Tseruïa, était [préposé] sur l’armée; et Josaphat, fils d’Akhilud, était rédacteur des chroniques;
17 Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
et Tsadok, fils d’Akhitub, et Akhimélec, fils d’Abiathar, étaient sacrificateurs; et Seraïa était scribe;
18 Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.
et Benaïa, fils de Jehoïada, [était chef] des Keréthiens et des Peléthiens; et les fils de David étaient les principaux officiers.