< 2 Sama’ila 8 >

1 Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
Some time later, David’s army attacked the Philistia [army] and defeated them. They took control over the entire Philistia area.
2 Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
David’s army also defeated the army of the Moab people-group. David forced their soldiers to lie down on the ground [close to each other]. His men killed two out of every three of them. The [other] Moab people [were forced to] accept David as their ruler, and they were forced to give to him [every year the] payment/tax [that he demanded].
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
David’s army also defeated [the army of] Hadadezer, the son of Rehob, who ruled [the state of] Zobah [in Syria]. That happened when David went to rule again over the area at [the upper part of] the Euphrates River.
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
David’s army captured 1,700 of Hadadezer’s soldiers who rode on horses, and 20,000 of his other soldiers. They also crippled/hamstrung most of the horses that pulled the chariots, but they left/spared enough horses to [pull] 100 chariots.
5 Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
When [the army of] Syria came from Damascus [city] to help King Hadadezer’s [army], David’s soldiers killed 22,000 of them.
6 Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Then David stationed (groups of his soldiers/army camps) in their area, and the people of Syria were forced to accept David as their ruler, and to give to David’s government [every year] the payment/tax that he demanded. And Yahweh enabled David’s [army] to win victories wherever they went.
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
David’s soldiers took the gold shields that were carried by Hadadezer’s officials, and brought them to Jerusalem.
8 Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
They also brought [to Jerusalem] a lot of bronze [that they found] in Betah and Berothai, two cities that King Hadadezer [had previously] ruled.
9 Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
When Toi, the king of the Hamath [city in Syria], heard that David’s [army] had defeated the entire army of King Hadadezer,
10 sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
he sent his son Joram to greet King David and to (congratulate him/say that he was happy) about his army defeating Hadadezer’s army, which Toi’s [army] had fought many times. Joram brought to David many items/gifts made from gold, silver, and bronze.
11 Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
King David dedicated all those items to Yahweh. He also dedicated the silver and gold which his army had taken from the nations that they had conquered.
12 wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
They had taken items from the Edom people-group and the Moab people-group, from the Ammon people-group, from the Philistia people, and from [the descendants of] Amalek, as well as from the people that Hadadezer [previously] ruled.
13 Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
When David returned [after defeating the armies of Syria], he became more famous because his army killed 18,000 soldiers from the Edom people-group in the Salt Valley [near the Dead Sea].
14 Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
David stationed (groups of his soldiers/army camps) throughout the Edom area, and forced the people there to accept him as their king. Yahweh enabled David’s [army] to win battles wherever they went.
15 Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
David ruled over all the Israeli people, and he always did for them what was fair and just.
16 Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
Joab was the army commander; Jehoshaphat, the son of Ahilud, was the man who reported to the people everything that David decided that they should do;
17 Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
Zadok the son of Ahitub and Ahimelech the son of Abiathar were the priests; Seraiah was the official secretary;
18 Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.
Benaiah the son of Jehoiada was the commander of (David’s bodyguards/the men who protected the king); and David’s sons were priests (OR, his administrators/advisors).

< 2 Sama’ila 8 >