< 2 Sama’ila 8 >

1 Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
And it comes to pass afterward that David strikes the Philistines, and humbles them, and David takes the bridle of the metropolis out of the hand of the Philistines.
2 Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
And he strikes Moab, and measures them with a line, causing them to lie down on the earth, and he measures two lines to put to death, and the fullness of the line to keep alive, and the Moabites are for servants to David, bearers of a present.
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
And David strikes Hadadezer son of Rehob, king of Zobah, in his going to bring back his power by the River [Euphrates];
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
and David captures from him one thousand and seven hundred horsemen, and twenty thousand footmen, and David utterly destroys the whole of the charioteers; he leaves only one hundred of their charioteers.
5 Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
And Aram of Damascus comes to give help to Hadadezer king of Zobah, and David strikes twenty-two thousand men of Aram;
6 Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
and David puts garrisons in Aram of Damascus, and Aram is for a servant to David, carrying a present; and YHWH saves David wherever he has gone;
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
and David takes the shields of gold which were on the servants of Hadadezer, and brings them to Jerusalem;
8 Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
and from Betah, and from Berothai, cities of Hadadezer, King David has taken very much bronze.
9 Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
And Toi king of Hamath hears that David has struck all the force of Hadadezer,
10 sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
and Toi sends his son Joram to King David to ask of him of welfare, and to bless him (because that he has fought against Hadadezer, and strikes him, for Hadadezer had been a man of wars [with] Toi), and in his hand have been vessels of silver, and vessels of gold, and vessels of bronze,
11 Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
also King David sanctified them to YHWH, with the silver and the gold which he sanctified of all the nations which he subdued:
12 wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
of Aram, and of Moab, and of the sons of Ammon, and of the Philistines, and of Amalek, and of the spoil of Hadadezer son of Rehob king of Zobah.
13 Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
And David makes a name in his turning back from his striking Aram in the Valley of Salt—eighteen thousand;
14 Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
and he puts garrisons in Edom—he has put garrisons in all of Edom, and all Edom are servants to David; and YHWH saves David wherever he has gone.
15 Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
And David reigns over all Israel, and David is doing judgment and righteousness to all his people,
16 Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
and Joab son of Zeruiah [is] over the host, and Jehoshaphat son of Ahilud [is] remembrancer,
17 Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
and Zadok son of Ahitub, and Ahimelech son of Abiathar, [are] priests, and Seraiah [is] scribe,
18 Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.
and Benaiah son of Jehoiada [is over] both the Cherethite and the Pelethite, and the sons of David have been ministers.

< 2 Sama’ila 8 >