< 2 Sama’ila 8 >
1 Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
Bangʼ kinde moko Daudi noloyo jo-Filistia ma gibedo e bwo lochne, kendo nokawo Metheg Ama mogolo e loch jo-Filistia.
2 Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
Daudi noloyo jo-Moab bende. Noketogi ma ginindo piny eka nopimogi gi tol. Kano pimogi diriyo to mago ninego to mane opim mar adek ne iweyo kangima. Omiyo jo-Moab nobedo e bwo loch Daudi kendo negigolone osuru.
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
Bende Daudi nokedo gi Hadadezer wuod Rehob, ma ruodh Zoba, eka nodhi mondo ogur lochne e dho Aora Yufrate.
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
Daudi nomako geche lweny alufu achiel gi joidh farese alufu abiriyo, gi jolweny mawuotho gi tiendgi alufu piero ariyo. Nongʼado odond farese duto.
5 Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
Kane jo-Aram moa Damaski obiro konyo Hadadezer ruodh Zoba, Daudi nonego ji alufu piero ariyo gariyo kuomgi.
6 Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Noketo kambi mag jolwenje e dala maduongʼ mar Damaski e piny jo-Aram kendo jo-Aram nobedo e bwo lochne kendo negikelone osuru. Jehova Nyasaye nomiyo Daudi olocho kamoro amora mane odhiye.
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
Daudi nokawo kuodi molos gi dhahabu mane mag jotend lweny mar Hadadezer, mi okelogi Jerusalem.
8 Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
Ruoth Daudi nokawo mula mogundho chakre Teba nyaka Berothai mane gin miech Hadadezer.
9 Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
Kane Tou ruodh Hamath owinjo ni Daudi noloyo jolweny duto mag Hadadezer,
10 sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
nooro wuode miluongo ni Joram ir Ruoth Daudi mondo omose kendo opake kuom loch moloyogo Hadadezer, manosebedo kakedo gi Tou. Joram nokelo gik molos gi fedha, dhahabu to gi mula.
11 Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
Ruoth Daudi nowalo gigi duto momiyo Jehova Nyasaye, mana kaka nosetimo gi fedha gi dhahabu mane oa kuom ogendini mane oloyo kaka:
12 wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
Edom gi Moab gi jo-Amon gi jo-Filistia, gi Amalek. E kaka nowalo bende gik mane oyaki mag Hadadezer wuod Rehob, ma ruodh Zoba.
13 Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
Kendo Daudi humbe nolandore koa nego jo-Edom alufu apar gaboro e Holo mar Chumbi.
14 Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
Bangʼe noketo kambi askeche e piny Edom duto, mi jo-Edom nobedo e bwo loch Daudi. Kamoro amora ma Daudi nodhiye Jehova Nyasaye nomiye loch.
15 Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
Daudi nobedo ruodh jo-Israel duto, kotimo maber kendo makare ni joge duto.
16 Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
Joab wuod Zeruya ne jatend jolweny; Jehoshafat wuod Ahilud ne jachan weche;
17 Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
Zadok wuod Ahitub gi Ahimelek wuod Abiathar ne jodolo; Seraya ne jagoro;
18 Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.
Benaya wuod Jehoyada ne jatend jo-Kereth gi jo-Peleth; to yawuot Daudi to ne jangʼad rieko mar joka ruoth.