< 2 Sama’ila 7 >

1 Bayan sarki ya kama zama a fadansa Ubangiji kuma ya hutashe shi daga dukan abokan gābansa da suke kewaye da shi,
Quando o rei vivia em sua casa, e Javé havia lhe dado descanso de todos os seus inimigos ao redor,
2 sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar katakon al’ul, amma akwatin alkawarin Allah yana zaune a tenti.”
o rei disse ao profeta Natan: “Veja agora, eu moro em uma casa de cedro, mas a arca de Deus mora dentro de cortinas”.
3 Natan ya amsa wa sarki ya ce, “Duk abin da yake a zuciyarka, sai ka yi, gama Ubangiji yana tare da kai.”
Nathan disse ao rei: “Vá, faça tudo o que está em seu coração, pois Yahweh está com você”.
4 A daren nan maganar Ubangiji ta zo wa Natan cewa,
Naquela mesma noite, a palavra de Javé veio a Nathan, dizendo:
5 “Je ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, kai ne za ka gina mini gida in zauna?
“Vá e diga ao meu servo David: 'Javé diz: 'Você deveria construir uma casa para eu morar?
6 Ban taɓa zama a gida ba tun daga ranar da na fito da Isra’ilawa daga Masar har yă zuwa yau. Ina dai kai da kawowa a tenti, a matsayin mazaunina.
Pois eu não vivo em uma casa desde o dia em que tirei os filhos de Israel do Egito, até hoje, mas me mudei em uma tenda e em um tabernáculo”.
7 A cikin kaiwa da kawowar da nake yi cikin dukan Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani shugabanninsu wanda na umarta su lura da mutanena Isra’ila, “Don me ba ku gina mini mazauni da katakon al’ul ba?”’
Em todos os lugares em que caminhei com todos os filhos de Israel, eu disse uma palavra a alguém das tribos de Israel a quem ordenei que fosse pastor de meu povo Israel, dizendo: 'Por que não me construiu uma casa de cedro?
8 “Yanzu, ka gaya wa bawana Dawuda ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauko ka daga makiyaya, daga kuma garken tumaki ka zama sarki bisan mutane Isra’ila.
Agora, portanto, diga isto ao meu servo David: Yahweh dos Exércitos diz: “Eu o tirei do curral de ovelhas, de seguir as ovelhas, para ser príncipe sobre meu povo, sobre Israel”.
9 Na kasance tare da kai duk inda ka tafi, na kuma kawar da dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka yă shahara kamar sunayen shahararrun mutanen duniya.
Eu estive com você onde quer que você tenha ido, e cortei todos os seus inimigos de antes de você”. Vou fazer de vocês um grande nome, como o nome dos grandes que estão na terra.
10 Zan kuma tanada wa mutanena Isra’ila wuri, in kuma dasa su yadda za su kasance da gida kansu ba tare da an ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara wahalshe su kamar dā ba,
Designarei um lugar para meu povo Israel, e o plantarei, para que ele possa morar em seu próprio lugar e não seja mais movido. Os filhos da maldade não os afligirão mais, como no início,
11 yadda suka yi tun lokacin da na naɗa shugabanni bisan mutanena Isra’ila, zan kuma hutashe ka daga hannun abokan gābanka. “‘Ubangiji ya furta maka cewa Ubangiji kansa zai kafa maka gida.
e a partir do dia em que ordenei aos juízes que estivessem sobre meu povo Israel. Farei com que descansem de todos os seus inimigos. Além disso, Javé lhe diz que Javé fará de você uma casa.
12 Sa’ad da kwanakinka suka ƙare, za ka huta tare da kakanninka, zan tā da zuriyarka, na cikinka, zan kuma sa mulkinsa ya kahu.
Quando seus dias estiverem cumpridos e você dormir com seus pais, eu farei com que seus descendentes venham atrás de você, que sairá de seu corpo, e estabelecerei seu reino.
13 Shi zai gina gida domin Sunana, zan kuwa kafa gadon sarautarsa har abada.
Ele construirá uma casa em meu nome, e eu estabelecerei o trono de seu reino para sempre.
14 Zan zama Ubansa, shi kuma yă zama ɗana. Idan ya yi laifi, zan yi amfani da mutane in hukunta shi. Mutane ne za su zama bulalata.
Eu serei seu pai, e ele será meu filho. Se ele cometer iniqüidade, castigá-lo-ei com a vara dos homens e com as listras dos filhos dos homens;
15 Amma ba za a taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi yadda na ɗauke ta daga wurin Shawulu ba, shi wannan wanda na kawar daga gabanka.
mas minha bondade amorosa não se afastará dele, como a tirei de Saul, a quem guardei diante de vós.
16 Gidanka da kuma masarautarka za su dawwama har abada a gabana; gadon sarautarka kuma zai kahu har abada.’”
Sua casa e seu reino serão assegurados para sempre diante de você. Vosso trono será estabelecido para sempre”'”.
17 Natan ya gaya wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.
Nathan falou a David todas estas palavras, e de acordo com toda esta visão.
18 Sa’an nan Sarki Dawuda ya je ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ko gidana, har da ka ɗaga mu zuwa wannan matsayi?
Então o rei David entrou e sentou-se diante de Javé; e disse: “Quem sou eu, Senhor Javé, e qual é a minha casa, que o Senhor me trouxe até aqui?
19 Har ya zama kamar wannan bai isa ba a gabanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka kuma yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Haka ka saba yi da mutane, ya Ubangiji Mai Iko Duka?
Isto ainda era uma coisa pequena aos seus olhos, Senhor Javé, mas você também falou da casa de seu servo por um grande tempo; e isto entre os homens, Senhor Javé!
20 “Me kuma Dawuda zai ce maka? Gama ka san bawanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka.
O que mais David pode dizer a você? Pois você conhece seu servo, Lorde Yahweh.
21 Gama saboda maganarka da kuma bisa ga nufinka, ka aikata wannan babban abu, ka kuma sanar da bawanka.
Por sua palavra, e de acordo com seu próprio coração, você trabalhou toda essa grandeza, para que seu servo a conhecesse.
22 “Kai mai girma ne, ya Ubangiji Mai Iko Duka! Babu wani kamar ka, babu kuma wani Allah sai kai; kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
Portanto, você é grande, Senhor Javé Deus. Pois não há ninguém como você, nem há outro Deus além de você, segundo tudo o que ouvimos com nossos ouvidos.
23 Wane ne kuma yake kamar da mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allah ya fita don yă kuɓutar wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa da kuma al’amuran banmamaki ta wurin korin al’ummai da allolinsu daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar daga Masar?
Que nação na terra é como teu povo, mesmo como Israel, que Deus foi resgatar para si mesmo por um povo, e fazer para si mesmo um nome, e fazer grandes coisas por ti, e coisas espantosas por tua terra, diante de teu povo, que resgataste para ti mesmo do Egito, das nações e de seus deuses?
24 Ka kafa mutanenka Isra’ila kamar naka na kanka har abada, kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
Você estabeleceu para si mesmo seu povo Israel para ser seu povo para sempre; e você, Javé, tornou-se o Deus deles.
25 “Yanzu kuwa, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa. Ka yi kamar yadda ka alkawarta,
“Agora, Javé Deus, a palavra que você falou a respeito de seu servo, e a respeito de sua casa, confirme-a para sempre, e faça como você falou.
26 domin sunanka yă kasance da girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah ne a bisa Isra’ila!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
Que seu nome seja eternamente engrandecido, dizendo: 'Javé dos Exércitos é Deus sobre Israel; e a casa de seu servo Davi será estabelecida diante de você'.
27 “Ya Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka bayyana wa bawanka cewa, ‘Zan gina maka gida.’ Saboda haka bawanka ya sami ƙarfin hali yă miƙa maka wannan addu’a.
Para você, Javé dos Exércitos, o Deus de Israel, revelou a seu servo, dizendo: 'Eu lhe construirei uma casa'. Portanto, seu servo encontrou em seu coração esta oração para rezar a você.
28 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai Allah ne! Maganarka da aminci take, ka kuma yi wa bawanka waɗannan abubuwa masu kyau.
“Agora, ó Senhor Javé, Vós sois Deus, e vossas palavras são verdade, e prometestes este bem a vosso servo.
29 In ya gamshe ka, bari ka albarkaci gidan bawanka don yă dawwama a gabanka har abada; gama kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka riga ka yi magana, kuma saboda kai ka sa albarka ga gidan bawanka, lalle zai kasance da albarka har abada.”
Agora, portanto, deixai que vos agrade abençoar a casa de vosso servo, para que ela continue para sempre diante de vós; pois vós, Senhor Javé, o dissestes. Que a casa de seu servo seja abençoada para sempre com a sua bênção”.

< 2 Sama’ila 7 >