< 2 Sama’ila 7 >
1 Bayan sarki ya kama zama a fadansa Ubangiji kuma ya hutashe shi daga dukan abokan gābansa da suke kewaye da shi,
Som nu kongen bodde i sitt hus, og Herren hadde latt ham få ro for alle hans fiender rundt omkring,
2 sai ya ce wa annabi Natan, “Ga ni, ina zama a fadar katakon al’ul, amma akwatin alkawarin Allah yana zaune a tenti.”
sa han til profeten Natan: Se, jeg bor i et hus av sedertre, mens Guds ark bor mellem telttepper.
3 Natan ya amsa wa sarki ya ce, “Duk abin da yake a zuciyarka, sai ka yi, gama Ubangiji yana tare da kai.”
Natan sa til kongen: Gjør du bare alt det du har i sinne! For Herren er med dig.
4 A daren nan maganar Ubangiji ta zo wa Natan cewa,
Men samme natt kom Herrens ord til Natan, og det lød således:
5 “Je ka faɗa wa bawana Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce, kai ne za ka gina mini gida in zauna?
Gå og si til min tjener David: Så sier Herren: Skulde du bygge mig et hus til å bo i?
6 Ban taɓa zama a gida ba tun daga ranar da na fito da Isra’ilawa daga Masar har yă zuwa yau. Ina dai kai da kawowa a tenti, a matsayin mazaunina.
Jeg har jo ikke bodd i hus like fra den dag jeg førte Israels barn op fra Egypten, og til denne dag, men jeg vandret om i et telt, i et tabernakel.
7 A cikin kaiwa da kawowar da nake yi cikin dukan Isra’ilawa, na taɓa ce wa wani shugabanninsu wanda na umarta su lura da mutanena Isra’ila, “Don me ba ku gina mini mazauni da katakon al’ul ba?”’
Hvor jeg så vandret om med alle Israels barn, har jeg vel nogensinne talt således til nogen av Israels stammer som jeg satte til å vokte mitt folk Israel: Hvorfor har I ikke bygget mig et hus av sedertre?
8 “Yanzu, ka gaya wa bawana Dawuda ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, na ɗauko ka daga makiyaya, daga kuma garken tumaki ka zama sarki bisan mutane Isra’ila.
Derfor skal du si således til min tjener David: Så sier Herren, hærskarenes Gud: Jeg tok dig fra havnegangen, hvor du gikk bak fårene, forat du skulde være fyrste over mitt folk Israel.
9 Na kasance tare da kai duk inda ka tafi, na kuma kawar da dukan abokan gābanka a gabanka. Yanzu zan sa sunanka yă shahara kamar sunayen shahararrun mutanen duniya.
Og jeg var med dig overalt hvor du gikk, og utryddet alle dine fiender for dig, og jeg har latt dig vinne et stort navn, så stort som de størstes navn på jorden.
10 Zan kuma tanada wa mutanena Isra’ila wuri, in kuma dasa su yadda za su kasance da gida kansu ba tare da an ƙara damunsu ba. Mugayen mutane ba za su ƙara wahalshe su kamar dā ba,
Og jeg har gjort i stand et bosted for mitt folk Israel, og jeg har plantet det der, så det bor i sitt hjem og ikke uroes mere, og urettferdige mennesker ikke plager det lenger som før,
11 yadda suka yi tun lokacin da na naɗa shugabanni bisan mutanena Isra’ila, zan kuma hutashe ka daga hannun abokan gābanka. “‘Ubangiji ya furta maka cewa Ubangiji kansa zai kafa maka gida.
like fra den dag jeg satte dommere over mitt folk Israel, og jeg har latt dig få ro for alle dine fiender. Og nu forkynner Herren dig at Herren vil bygge dig et hus.
12 Sa’ad da kwanakinka suka ƙare, za ka huta tare da kakanninka, zan tā da zuriyarka, na cikinka, zan kuma sa mulkinsa ya kahu.
Når dine dagers tall er fullt, og du hviler hos dine fedre, da vil jeg efter dig opreise din sønn som skal utgå av ditt liv, og jeg vil grunnfeste hans kongedømme.
13 Shi zai gina gida domin Sunana, zan kuwa kafa gadon sarautarsa har abada.
Han skal bygge et hus for mitt navn, og jeg vil trygge hans kongetrone til evig tid.
14 Zan zama Ubansa, shi kuma yă zama ɗana. Idan ya yi laifi, zan yi amfani da mutane in hukunta shi. Mutane ne za su zama bulalata.
Jeg vil være hans far, og han skal være min sønn. Når han gjør det som ondt er, vil jeg tukte ham med menneskers ris og med menneskebarns plager;
15 Amma ba za a taɓa ɗauke ƙaunata daga gare shi yadda na ɗauke ta daga wurin Shawulu ba, shi wannan wanda na kawar daga gabanka.
men min miskunnhet skal ikke vike fra ham, således som jeg lot den vike fra Saul, han som jeg lot vike for dig.
16 Gidanka da kuma masarautarka za su dawwama har abada a gabana; gadon sarautarka kuma zai kahu har abada.’”
Fast skal ditt hus og ditt kongedømme stå til evig tid for ditt åsyn; din trone skal være grunnfestet til evig tid.
17 Natan ya gaya wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.
Alle disse ord og hele dette syn bar Natan frem for David.
18 Sa’an nan Sarki Dawuda ya je ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ko gidana, har da ka ɗaga mu zuwa wannan matsayi?
Da gikk kong David inn og blev der inne for Herrens åsyn, og han sa: Hvem er jeg, Herre, Herre, og hvad er mitt hus, at du har ført mig hertil?
19 Har ya zama kamar wannan bai isa ba a gabanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka kuma yi magana game da nan gaba na gidan bawanka. Haka ka saba yi da mutane, ya Ubangiji Mai Iko Duka?
Og enda var dette for lite i dine øine, Herre, Herre, og du talte også om din tjeners hus langt frem i tiden. Og dette er loven for menneskene, Herre, Herre!
20 “Me kuma Dawuda zai ce maka? Gama ka san bawanka, ya Ubangiji Mai Iko Duka.
Hvad skal så David mere si til dig? Du kjenner jo din tjener, Herre, Herre!
21 Gama saboda maganarka da kuma bisa ga nufinka, ka aikata wannan babban abu, ka kuma sanar da bawanka.
For ditt ords skyld og efter ditt hjerte har du gjort alt dette store og forkynt det for din tjener.
22 “Kai mai girma ne, ya Ubangiji Mai Iko Duka! Babu wani kamar ka, babu kuma wani Allah sai kai; kamar yadda muka ji da kunnuwanmu.
Derfor er du stor, Herre Gud! Det er ingen som du, og det er ingen Gud foruten dig, efter alt det vi har hørt med våre ører.
23 Wane ne kuma yake kamar da mutanenka Isra’ila, al’umma guda a duniya wadda Allah ya fita don yă kuɓutar wa kansa, ya kuma yi suna wa kansa, ya kuma aikata manyan abubuwa da kuma al’amuran banmamaki ta wurin korin al’ummai da allolinsu daga gaban mutanenka, waɗanda ka kuɓutar daga Masar?
Og hvor er det på jorden et eneste folk som ditt folk - som Israel - et folk som Gud kom og fridde ut, så det skulde være hans eget folk, for å gjøre sig et navn og for å gjøre dette store for eder og forferdelige gjerninger for ditt land, for ditt folks skyld som du fridde ut fra Egypten, fra hedningefolk og deres guder?
24 Ka kafa mutanenka Isra’ila kamar naka na kanka har abada, kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu.
Og du dannet dig ditt folk Israel, så det skulde være ditt folk til evig tid, og du, Herre, er blitt deres Gud.
25 “Yanzu kuwa, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi game da bawanka da gidansa. Ka yi kamar yadda ka alkawarta,
Så opfyll nu, Herre Gud, for evig tid det ord du har talt over din tjener og hans hus, og gjør som du har sagt!
26 domin sunanka yă kasance da girma har abada. Sa’an nan mutane za su ce, ‘Ubangiji Maɗaukaki, Allah ne a bisa Isra’ila!’ Kuma gidan bawanka Dawuda zai kahu a gabanka.
Da skal ditt navn bli stort til evig tid, så folk skal si: Herren, hærskarenes Gud, er Gud over Israel. Og din tjener Davids hus skal være grunnfestet for ditt åsyn.
27 “Ya Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, ka bayyana wa bawanka cewa, ‘Zan gina maka gida.’ Saboda haka bawanka ya sami ƙarfin hali yă miƙa maka wannan addu’a.
For du, Herre, hærskarenes Gud, Israels Gud, har åpenbaret for din tjener at du vil bygge mig et hus. Derfor har din tjener fått frimodighet til å bede denne bønn til dig.
28 Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai Allah ne! Maganarka da aminci take, ka kuma yi wa bawanka waɗannan abubuwa masu kyau.
Og nu, Herre, Herre, du er Gud, og dine ord skal bli sannhet, og du har lovt din tjener denne lykke.
29 In ya gamshe ka, bari ka albarkaci gidan bawanka don yă dawwama a gabanka har abada; gama kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka riga ka yi magana, kuma saboda kai ka sa albarka ga gidan bawanka, lalle zai kasance da albarka har abada.”
Så la det nu behage dig å velsigne din tjeners hus, så det må bli stående for ditt åsyn til evig tid! For du, Herre, Herre, har talt, og for din velsignelses skyld skal din tjeners hus bli velsignet i all evighet.