< 2 Sama’ila 6 >

1 Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
David je ponovno zbral skupaj vse izbrane može iz Izraela, trideset tisoč.
2 Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
In David je vstal in z vsem ljudstvom, ki je bilo z njim, odšel od Baále Judove, da od tam prinese gor Božjo skrinjo, katere ime je imenovano po imenu Gospoda nad bojevniki, ki prebiva med kerubi.
3 Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
Božjo skrinjo so postavili na nov voz in jo privedli iz Abinadábove hiše, ki je bila v Gíbei. Abinadábova sinova Uzá in Ahjó pa sta gnala nov voz.
4 da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
Prinesli so jo iz Abinadábove hiše, ki je bila v Gíbei, spremljajoč Božjo skrinjo in Ahjó je šel pred skrinjo.
5 Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
David in vsa Izraelova hiša pa so igrali pred Gospodom na vse vrste glasbil, narejenih iz cipresovega lesa, celo na harfe, na plunke, na tamburine, na kornéte in na cimbale.
6 Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
In ko so prišli do Nahónovega mlatišča, je Uzá iztegnil svojo roko k Božji skrinji in jo prijel, kajti voli so jo tresli.
7 Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
Gospodova jeza je bila vžgana zoper Uzája in Bog ga je tam udaril zaradi njegove napake; in tam je umrl, ob Božji skrinji.
8 Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
David je bil razžaljen, ker je Gospod naredil vrzel nad Uzájem, in ime tega mesta je imenoval Perec Uzá do tega dne.
9 Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
David se je tisti dan zbal Gospoda in rekel: »Kako bo Gospodova skrinja prišla k meni?«
10 Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
Tako David Gospodove skrinje ni hotel prestaviti k sebi v Davidovo mesto, temveč jo je David odvedel vstran, v hišo Gitéjca Obéd Edóma.
11 Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
In Gospodova skrinja je tri mesece ostala v hiši Gitéjca Obéd Edóma in Gospod je blagoslovil Obéd Edóma in vso njegovo družino.
12 To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
To je bilo sporočeno kralju Davidu, rekoč: » Gospod je zaradi Božje skrinje blagoslovil hišo Obéd Edóma in vse, kar mu pripada.« Tako je David šel in z veseljem prinesel gor Božjo skrinjo iz hiše Obéd Edóma v Davidovo mesto.
13 Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
In bilo je tako, da ko so tisti, ki so nosili Gospodovo skrinjo, naredili šest korakov, je žrtvoval vole in pitance.
14 Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
David je z vso svojo močjo plesal pred Gospodom in David je bil opasan z lanenim efódom.
15 yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
Tako so David in vsa Izraelova hiša z vriskanjem in z zvokom šofarja Gospodovo skrinjo prinesli gor.
16 Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
Ko je Gospodova skrinja prišla v Davidovo mesto, je Savlova hči Mihála pogledala skozi okno in videla kralja Davida skakati in plesati pred Gospodom in ga prezirala v svojem srcu.
17 Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
In prinesli so Gospodovo skrinjo in jo postavili na njen kraj, v sredo šotorskega svetišča, ki ga je David razpel zanjo in David je pred Gospodom daroval žgalne daritve in mirovne daritve.
18 Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
Takoj, ko je David prenehal darovati žgalne daritve in mirovne daritve, je v imenu Gospoda nad bojevniki blagoslovil ljudstvo.
19 Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
Med vse ljudstvo je razdelil, celó med celotno Izraelovo množico, tako ženskam kakor moškim, vsakomur kolač kruha, dober kos mesa in flaškon vina. Tako je vse ljudstvo odšlo vsak k svoji hiši.
20 Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
Potem se je David vrnil, da blagoslovi svojo družino. Savlova hči Mihála pa je prišla ven, da sreča Davida in rekla: »Kako veličasten je bil danes Izraelov kralj, ki se je danes razkril pred očmi pomočnic svojih služabnikov, kakor se brezsramno razkriva nekdo izmed nadutih pajdašev.«
21 Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
David je rekel Miháli: » To je bilo pred Gospodom, ki me je izbral pred tvojim očetom in pred vso njegovo hišo, da me določi [za] vladarja nad Gospodovim ljudstvom, nad Izraelom. Zato bom igral pred Gospodom.
22 Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
In še bolj se bom pomanjšal kakor to in bom ponižen v svojem lastnem pogledu. Glede dekel pa, o katerih si govorila, od njih bom imel spoštovanje.«
23 Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.
Zato Savlova hči Mihála ni imela nobenega otroka do dneva svoje smrti.

< 2 Sama’ila 6 >