< 2 Sama’ila 6 >

1 Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
David assembla encore tous les hommes d'élite d'Israël, [qui furent] trente mille [hommes].
2 Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
Puis David se leva et partit avec tout le peuple qui était avec lui vers Bahalé de Juda, pour transporter l'Arche de Dieu, duquel le nom est appelé: Le nom de l'Eternel des armées, qui habite entre les Chérubins sur l'Arche.
3 Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
Et ils mirent l'Arche de Dieu sur un chariot tout neuf, et l'emmenèrent de la maison d'Abinadab, qui était au coteau; et Huza et Ahjo, enfants d'Abinadab, conduisaient le chariot neuf.
4 da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
Et ils l'emmenèrent, savoir l'Arche de Dieu de la maison d'Abinadab, qui était au coteau, et Ahjo allait devant l'Arche.
5 Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
Et David et toute la maison d'Israël jouaient devant l'Eternel de toutes sortes [d'instruments faits] de bois de sapin, et des violons, des musettes, des tambours, des sistres, et des cymbales.
6 Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
Et quand ils furent venus jusqu'à l'aire de Nacon, Huza porta [sa main] à l'Arche de Dieu, et la retint, parce que les bœufs avaient glissé.
7 Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
Et la colère de l'Eternel s'enflamma contre Huza, et Dieu le frappa là à cause de son indiscrétion, et il mourut là près de l'Arche de Dieu.
8 Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
Et David fut affligé de ce que l'Eternel avait fait brèche en [la personne] de Huza; c'est pourquoi on a appelé ce lieu-là jusqu'à aujourd'hui Pérets-Huza.
9 Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
Et David eut peur de l'Eternel en ce jour-là, et dit: Comment l'Arche de l'Eternel entrerait-elle chez moi?
10 Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
Et David ne voulut point retirer l'Arche de l'Eternel chez soi en la Cité de David, mais il la fit détourner en la maison d'Hobed-Edom Guittien.
11 Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
Et l'Arche de l'Eternel demeura trois mois en la maison d'Hobed-Edom Guittien; et l'Eternel bénit Hobed-Edom, et toute sa maison.
12 To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
Depuis on vint dire à David: L'Eternel a béni la maison d'Hobed-Edom, et tout ce qui lui appartient, pour l'amour de l'Arche de Dieu; c'est pourquoi David s'en alla, et amena l'Arche de Dieu de la maison d'Hobed-Edom, en la Cité de David, avec joie.
13 Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
Et il arriva que quand ceux qui portaient l'Arche de Dieu eurent marche six pas, on sacrifia des taureaux et des béliers gras.
14 Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
Et David sautait de toute sa force devant l'Eternel; et il était ceint d'un Ephod de lin.
15 yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
Ainsi David et toute la maison d'Israël menaient l'Arche de l'Eternel avec des cris de joie, et au son des trompettes.
16 Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
Mais comme l'Arche de l'Eternel entrait dans la Cité de David, Mical fille de Saül, regardant par la fenêtre, vit le Roi David sautant de toute sa force devant l'Eternel, et elle le méprisa en son cœur.
17 Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
Ils emmenèrent donc l'Arche de l'Eternel, et la posèrent en son lieu, dans un Tabernacle que David lui avait tendu. Et David offrit des holocaustes et des sacrifices de prospérités devant l'Eternel.
18 Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
Quand David eut achevé d'offrir des holocaustes et des sacrifices de prospérités, il bénit le peuple au nom de l'Eternel des armées.
19 Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
Et il partagea à tout le peuple, [savoir] à toute la multitude d'Israël, tant aux hommes qu'aux femmes, à chacun un gâteau, une pièce de chair, et une bouteille [de vin]; et tout le peuple s'en retourna chacun en sa maison.
20 Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
Puis David s'en retourna pour bénir sa maison; et Mical fille de Saül vint au-devant de lui, et lui dit: Que le Roi d'Israël s'est fait aujourd'hui un grand honneur en se découvrant aujourd'hui devant les yeux des servantes de ses serviteurs, comme ferait un homme de néant, sans en avoir honte!
21 Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
Et David dit à Mical: Ç'a été devant l'Eternel, qui m'a choisi plutôt que ton père, et que toute sa maison, et qui m'a commandé d'être le Conducteur de son peuple d'Israël; c'est pourquoi je me réjouirai devant l'Eternel.
22 Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
Et je me rendrai encore plus abject que [je n'ai fait] cette fois, et je m'estimerai encore moins; malgré cela je serai honoré devant les servantes dont tu as parlé.
23 Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.
Or Mical fille de Saül n'eut point d'enfants jusqu'au jour de sa mort.

< 2 Sama’ila 6 >