< 2 Sama’ila 6 >

1 Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
David rassembla de nouveau toute l’élite d’Israël, trente mille hommes,
2 Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
et, suivi de tout ce peuple, il se mit en marche du côté de Baalé-Yehouda pour en faire venir l’arche du Seigneur, à laquelle est imposé le nom, le nom même de l’Eternel-Cebaot, qui siège sur les chérubins.
3 Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
On plaça l’arche du Seigneur sur un chariot neuf, et on la transporta hors de la maison d’Abinadab, située sur la colline; Ouzza et Ahyo, fils d’Abinadab, conduisaient ce chariot neuf.
4 da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
Ils la voiturèrent depuis la maison d’Abinadab, située sur la colline, en accompagnant l’arche du Seigneur; mais Ahyo marchait en avant de l’arche.
5 Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
David et toute la maison d’Israël jouaient, devant le Seigneur, de toutes sortes d’instruments de bois de cyprès: harpes, luths, tambourins, sistres et cymbales.
6 Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
Comme on arrivait à l’aire de Nakhôn, Ouzza s’élança vers l’arche du Seigneur et la retint, parce que les bœufs avaient glissé.
7 Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
La colère du Seigneur s’alluma contre Ouzza, et il le frappa sur place pour cette faute; et il mourut là, à côté de l’arche de Dieu.
8 Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
David, consterné du coup dont l’Eternel avait frappé Ouzza, donna à ce lieu le nom de Péreç-Ouzza, qu’il porte encore aujourd’hui.
9 Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
David, ce jour-là, redouta l’Eternel et dit: "Comment l’arche de l’Eternel viendrait-elle chez moi!"
10 Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
Et David n’osa faire amener chez lui, dans la Cité de David, l’arche du Seigneur, et il la fit diriger vers la maison d’Obed-Edom, le Ghittéen.
11 Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
L’Arche du Seigneur demeura trois mois dans la maison d’Obed-Edom, le Ghittéen, et le Seigneur bénit Obed-Edom et toute sa maison.
12 To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
Le roi David, ayant appris que le Seigneur avait béni la maison et tous les biens d’Obed-Edom à cause de l’arche divine, y alla, et fit transporter l’arche divine de la maison d’Obéd-Edom à la Cité de David, avec des réjouissances.
13 Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
Quand ceux qui portaient l’arche du Seigneur avaient avancé de six pas, on immolait un taureau et une bête grasse.
14 Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
David dansait de toutes ses forces devant le Seigneur; il était vêtu d’un éphod de lin.
15 yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
Et David et toute la maison d’Israël escortaient l’arche du Seigneur avec des cris de joie et au son du cor.
16 Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
Comme l’arche du Seigneur entrait dans la Cité de David, Mikhal, fille de Saül, regarda par la fenêtre, vit le roi David sautant et dansant devant le Seigneur, et elle en conçut du dédain pour lui.
17 Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
Or, on introduisit l’arche du Seigneur et on l’installa à sa place, dans le pavillon que David avait dressé pour elle; et David offrit, devant l’Eternel, des holocaustes et des rémunératoires.
18 Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
Lorsque David eut achevé d’offrir ces sacrifices, il bénit le peuple au nom de l’Eternel-Cebaot,
19 Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
fit distribuer à tout le peuple, à toute la multitude d’Israël, hommes et femmes, à chacun un gâteau de pain, une pièce de viande et une mesure de vin; et tout le peuple se retira, chacun chez soi.
20 Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
David rentra pour bénir sa famille; Mikhal, fille de Saül, vint à sa rencontre et dit: "Combien s’est honoré aujourd’hui le roi d’Israël, se donnant en spectacle aux servantes de ses serviteurs, comme eût pu le faire un homme de rien!"
21 Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
David répondit à Mikhal: "C’Est devant l’Eternel, qui m’a élu de préférence à ton père et à tous les siens, en m’instituant prince du peuple de Dieu, prince d’Israël, c’est devant l’Eternel que j’ai dansé et danserai encore;
22 Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
et volontiers je m’humilierai davantage et me ferai petit à mes propres yeux; pour ces servantes dont tu parles, c’est auprès d’elles que je me glorifierai!"
23 Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.
Mikhal, fille de Saül, n’eut pas d’enfant jusqu’au jour de sa mort.

< 2 Sama’ila 6 >