< 2 Sama’ila 6 >

1 Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
And David again gathered together all the chosen men of Israel, thirty thousand.
2 Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
And David arose, and went with all the people who were with him, from Baale-judah, to bring up from there the ark of God, which is called by the Name, even the name of Jehovah of hosts who sits above the cherubim.
3 Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
And they set the ark of God upon a new cart, and brought it out of the house of Abinadab that was on the hill. And Uzzah and Ahio, the sons of Abinadab, drove the new cart.
4 da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
And they brought it out of the house of Abinadab, which was on the hill, with the ark of God, and Ahio went before the ark.
5 Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
And David and all the house of Israel played before Jehovah with all manner of instruments of fir-wood, and with harps, and with psalteries, and with timbrels, and with castanets, and with cymbals.
6 Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
And when they came to the threshing-floor of Nacon, Uzzah put forth to the ark of God, and took hold of it, for the oxen stumbled.
7 Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
And the anger of Jehovah was kindled against Uzzah, and God smote him there for his error, and he died there by the ark of God.
8 Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
And David was displeased, because Jehovah had broken forth upon Uzzah. And he called that place Perez-uzzah, to this day.
9 Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
And David was afraid of Jehovah that day, and he said, How shall the ark of Jehovah come to me?
10 Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
So David would not remove the ark of Jehovah to him into the city of David, but David carried it aside into the house of Obed-edom the Gittite.
11 Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
And the ark of Jehovah remained in the house of Obed-edom the Gittite three months, and Jehovah blessed Obed-edom, and all his house.
12 To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
And it was told king David, saying, Jehovah has blessed the house of Obed-edom, and all that pertains to him, because of the ark of God. And David went and brought up the ark of God from the house of Obed-edom into the city of David with joy.
13 Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
And it was so, that, when those who bore the ark of Jehovah had gone six paces, he sacrificed an ox and a fatling.
14 Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
And David danced before Jehovah with all his might. And David was girded with a linen ephod.
15 yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
So David and all the house of Israel brought up the ark of Jehovah with shouting, and with the sound of the trumpet.
16 Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
And it was so, as the ark of Jehovah came into the city of David, that Michal the daughter of Saul looked out at the window, and saw king David leaping and dancing before Jehovah, and she despised him in her heart.
17 Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
And they brought in the ark of Jehovah, and set it in its place, in the midst of the tent that David had pitched for it. And David offered burnt offerings and peace offerings before Jehovah.
18 Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
And when David had made an end of offering the burnt offering and the peace offerings, he blessed the people in the name of Jehovah of hosts.
19 Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
And he dealt among all the people, even among the whole multitude of Israel, both to men and women, to every one a cake of bread, and a portion of flesh, and a cake of raisins. So all the people departed every one to his house.
20 Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
Then David returned to bless his household. And Michal the daughter of Saul came out to meet David, and said, How glorious was the king of Israel today, who uncovered himself today in the eyes of the handmaids of his servants as one of the vain fellows shamelessly uncovers himself!
21 Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
And David said to Michal, It was before Jehovah, who chose me above thy father, and above all his house, to appoint me prince over the people of Jehovah, over Israel. Therefore I will play before Jehovah.
22 Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
And I will be yet more vile than this, and will be base in my own sight, but of the handmaids of whom thou have spoken, of them I shall be had in honor.
23 Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.
And Michal the daughter of Saul had no child to the day of her death.

< 2 Sama’ila 6 >