< 2 Sama’ila 5 >

1 Dukan kabilar Isra’ila suka zo wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu nama da jininka ne.
İsrail'in bütün oymakları Hevron'da bulunan Davut'a gelip şöyle dediler: “Biz senin etin, kemiğiniz.
2 A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’”
Geçmişte Saul kralımızken, savaşta İsrail'e komuta eden sendin. RAB sana, ‘Halkım İsrail'i sen güdecek, onlara sen önder olacaksın’ diye söz verdi.”
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, sarki ya yi yarjejjeniya da su a gaban Ubangiji, suka kuwa naɗa Dawuda sarki bisa Isra’ila.
İsrail'in bütün ileri gelenleri Hevron'a, Kral Davut'un yanına gelince, kral RAB'bin önünde orada onlarla bir antlaşma yaptı. Onlar da Davut'u İsrail Kralı olarak meshettiler.
4 Dawuda yana da shekara talatin ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara arba’in.
Davut otuz yaşında kral oldu ve kırk yıl krallık yaptı.
5 A Hebron ya yi mulki a bisa Yahuda shekara bakwai da wata shida, a Urushalima kuma ya yi mulki a bisa Isra’ila da Yahuda shekara talatin da uku.
Hevron'da yedi yıl altı ay Yahuda'ya, Yeruşalim'de otuz üç yıl bütün İsrail'e ve Yahuda'ya krallık yaptı.
6 Sarki da mutanensa suka tafi Urushalima don su kai wa Yebusiyawan da suke zaune a can hari, Yebusiyawa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba; ko makafi da guragu kaɗai ma za su kore ka.” Suka yi tsammani suna cewa, “Dawuda ba zai iya shiga can ba.”
Kral Davut'la adamları Yeruşalim'de yaşayan Yevuslular'a saldırmak için yola çıktılar. Yevuslular Davut'a, “Sen buraya giremezsin, körlerle topallar bile seni geri püskürtebilir” dediler. “Davut buraya giremez” diye düşünüyorlardı.
7 Duk da haka, Dawuda ya kame kagarar Sihiyona, wadda ta zama Birnin Dawuda.
Ne var ki, Davut Siyon Kalesi'ni ele geçirdi. Daha sonra bu kaleye “Davut Kenti” adı verildi.
8 A ranar, Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kame Yebusiyawa, dole yă yi amfani da wuriyar ruwa don yă kai ga waɗannan ‘guragu da makafi’ waɗanda suke abokan gāban Dawuda.” Shi ya sa suka ce, “‘Makafi da guragu’ ba za su shiga fadan sarki ba.”
Davut o gün adamlarına şöyle demişti: “Yevuslular'ı kim yenilgiye uğratırsa Davut'un nefret ettiği şu ‘Topallarla körlere’ su kanalından ulaşmalı!” “Körlerle topallar saraya giremeyecek” denmesinin nedeni işte budur.
9 Sai Dawuda ya zauna a kagarar, ya kuma kira ta Birnin Dawuda. Ya gina wuraren da suke kewaye da ita, tun daga madogaran gini zuwa ciki.
Bundan sonra Davut “Davut Kenti” adını verdiği kalede oturmaya başladı. Çevredeki bölgeyi, Millo'dan içeriye doğru uzanan bölümü inşa etti.
10 Ya yi ta ƙara ƙarfi, gama Ubangiji Allah Maɗaukaki yana tare da shi.
Davut giderek güçleniyordu. Çünkü Her Şeye Egemen Tanrı RAB onunlaydı.
11 To, Hiram sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda tare da gumaguman itacen al’ul, da kafintoci, da kuma maginan duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda fada.
Sur Kralı Hiram Davut'a ulaklar, sedir kütükleri, marangozlar ve taşçılar gönderdi. Bu adamlar Davut için bir saray yaptılar.
12 Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya naɗa shi sarki bisa Isra’ila, ya kuma ɗaukaka masarautarsa saboda mutanensa Isra’ila.
Böylece Davut RAB'bin kendisini İsrail Kralı atadığını ve halkı İsrail'in hatırı için krallığını yücelttiğini anladı.
13 Bayan ya bar Hebron, Dawuda ya ƙara ɗauko wa kansa waɗansu ƙwarƙwarai da mata a Urushalima. Aka haifa masa’ya’ya maza da mata.
Davut Hevron'dan ayrıldıktan sonra Yeruşalim'de kendine daha birçok cariye ve karı aldı. Davut'un erkek ve kız çocukları oldu.
14 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
Davut'un Yeruşalim'de doğan çocuklarının adları şunlardı: Şammua, Şovav, Natan, Süleyman,
15 Ibhar, Elishuwa, Nefeg, Yafiya,
Yivhar, Elişua, Nefek, Yafia,
16 Elishama, Eliyada da Elifelet.
Elişama, Elyada ve Elifelet.
17 Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
Filistliler Davut'un İsrail Kralı olarak meshedildiğini duyunca, bütün Filist ordusu onu aramak için yola çıktı. Bunu duyan Davut kaleye sığındı.
18 To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
Filistliler gelip Refaim Vadisi'ne yayılmışlardı.
19 saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
Davut RAB'be danıştı: “Filistliler'e saldırayım mı? Onları elime teslim edecek misin?” RAB Davut'a, “Saldır” dedi, “Onları kesinlikle eline teslim edeceğim.”
20 Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
Bunun üzerine Davut Baal-Perasim'e gidip orada Filistliler'i bozguna uğrattı. Sonra, “Her şeyi yarıp geçen sular gibi, RAB düşmanlarımı önümden yarıp geçti” dedi. Bundan ötürü oraya Baal-Perasim adı verildi.
21 Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
Davut'la adamları, Filistliler'in orada bıraktığı putları alıp götürdüler.
22 Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;
Filistliler bir kez daha gelip Refaim Vadisi'ne yayıldılar.
23 saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.
Davut RAB'be danıştı. RAB şöyle karşılık verdi: “Buradan saldırma! Onları arkadan çevirip pelesenk ağaçlarının önünden saldır.
24 Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”
Pelesenk ağaçlarının tepesinden yürüyüş sesi duyar duymaz, acele et. Çünkü ben Filist ordusunu bozguna uğratmak için önünsıra gitmişim demektir.”
25 Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.
Davut RAB'bin kendisine buyurduğu gibi yaptı ve Filistliler'i Geva'dan Gezer'e kadar bozguna uğrattı.

< 2 Sama’ila 5 >