< 2 Sama’ila 5 >

1 Dukan kabilar Isra’ila suka zo wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu nama da jininka ne.
Então todas as tribos de Israel vieram a David em Hebron e falaram, dizendo: “Eis que somos teus ossos e tua carne”.
2 A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’”
Em tempos passados, quando Saul era rei sobre nós, foi você quem conduziu Israel para fora e para dentro. Javé lhe disse: “Você será pastor do meu povo Israel, e você será príncipe sobre Israel”.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, sarki ya yi yarjejjeniya da su a gaban Ubangiji, suka kuwa naɗa Dawuda sarki bisa Isra’ila.
Então todos os anciãos de Israel vieram ao rei em Hebron, e o rei Davi fez um pacto com eles em Hebron antes de Yavé; e ungiram Davi rei sobre Israel.
4 Dawuda yana da shekara talatin ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara arba’in.
David tinha trinta anos de idade quando começou a reinar, e reinou quarenta anos.
5 A Hebron ya yi mulki a bisa Yahuda shekara bakwai da wata shida, a Urushalima kuma ya yi mulki a bisa Isra’ila da Yahuda shekara talatin da uku.
Em Hebron reinou sobre Judá sete anos e seis meses, e em Jerusalém reinou trinta e três anos sobre todo Israel e Judá.
6 Sarki da mutanensa suka tafi Urushalima don su kai wa Yebusiyawan da suke zaune a can hari, Yebusiyawa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba; ko makafi da guragu kaɗai ma za su kore ka.” Suka yi tsammani suna cewa, “Dawuda ba zai iya shiga can ba.”
O rei e seus homens foram a Jerusalém contra os jebuseus, os habitantes da terra, que falaram com Davi, dizendo: “Os cegos e os coxos te manterão fora daqui”, pensando: “Davi não pode entrar aqui”.
7 Duk da haka, Dawuda ya kame kagarar Sihiyona, wadda ta zama Birnin Dawuda.
Nevertheless David tomou o bastião de Sião. Esta é a cidade de Davi.
8 A ranar, Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kame Yebusiyawa, dole yă yi amfani da wuriyar ruwa don yă kai ga waɗannan ‘guragu da makafi’ waɗanda suke abokan gāban Dawuda.” Shi ya sa suka ce, “‘Makafi da guragu’ ba za su shiga fadan sarki ba.”
David disse naquele dia: “Quem quer que atinja os jebusitas, deixe-o subir ao curso de água e atinja aqueles cegos e coxos, que são odiados pela alma de David”. Portanto, eles dizem: “Os cegos e os coxos não podem entrar na casa”.
9 Sai Dawuda ya zauna a kagarar, ya kuma kira ta Birnin Dawuda. Ya gina wuraren da suke kewaye da ita, tun daga madogaran gini zuwa ciki.
David viveu na fortaleza, e a chamou de cidade de David. David construiu em torno de Millo e para dentro.
10 Ya yi ta ƙara ƙarfi, gama Ubangiji Allah Maɗaukaki yana tare da shi.
David cresceu cada vez mais, pois Yahweh, o Deus dos Exércitos, estava com ele.
11 To, Hiram sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda tare da gumaguman itacen al’ul, da kafintoci, da kuma maginan duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda fada.
Hiram, rei de Tiro, enviou mensageiros a Davi, com cedros, carpinteiros e pedreiros; e eles construíram uma casa para Davi.
12 Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya naɗa shi sarki bisa Isra’ila, ya kuma ɗaukaka masarautarsa saboda mutanensa Isra’ila.
David percebeu que Javé o havia estabelecido rei sobre Israel, e que ele havia exaltado seu reino por causa de seu povo Israel.
13 Bayan ya bar Hebron, Dawuda ya ƙara ɗauko wa kansa waɗansu ƙwarƙwarai da mata a Urushalima. Aka haifa masa’ya’ya maza da mata.
David levou mais concubinas e esposas para fora de Jerusalém, depois de ter vindo de Hebron; e mais filhos e filhas nasceram para David.
14 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
Estes são os nomes daqueles que nasceram para ele em Jerusalém: Shammua, Shobab, Nathan, Salomão,
15 Ibhar, Elishuwa, Nefeg, Yafiya,
Ibhar, Elishua, Nepheg, Japhia,
16 Elishama, Eliyada da Elifelet.
Elishama, Eliada, e Eliphelet.
17 Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
Quando os filisteus ouviram que tinham ungido Davi rei sobre Israel, todos os filisteus subiram em busca de Davi, mas Davi ouviu falar disso e desceu para a fortaleza.
18 To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
Agora os filisteus tinham vindo e se espalhado pelo vale de Rephaim.
19 saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
Davi perguntou a Javé, dizendo: “Devo eu ir contra os filisteus? Você vai entregá-los em minhas mãos?” Yahweh disse a David: “Suba; pois certamente entregarei os filisteus em suas mãos”.
20 Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
David veio a Baal Perazim, e David os atingiu lá. Então ele disse: “Yahweh quebrou meus inimigos diante de mim, como a brecha das águas”. Portanto, ele chamou o nome daquele lugar de Baal Perazim.
21 Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
Eles deixaram suas imagens lá, e David e seus homens os levaram embora.
22 Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;
Os filisteus surgiram mais uma vez e se espalharam pelo vale do Rephaim.
23 saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.
Quando David perguntou sobre Yahweh, ele disse: “Você não deve subir. Dêem a volta por trás deles e os ataquem na frente das amoras.
24 Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”
Quando ouvir o som de marcha nas copas das amoras, então se agita; pois então Javé saiu diante de você para atacar o exército dos filisteus”.
25 Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.
David o fez, como lhe ordenou Yahweh, e atingiu os filisteus durante todo o caminho de Geba a Gezer.

< 2 Sama’ila 5 >