< 2 Sama’ila 5 >

1 Dukan kabilar Isra’ila suka zo wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu nama da jininka ne.
Så kom alle Israels stammer til David i Hebron og sa: Her er vi; vi er av samme kjød og blod som du.
2 A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’”
Allerede for lenge siden, da Saul var konge over oss, var det du som førte Israel ut og inn, og Herren sa til dig: Du skal vokte mitt folk Israel, og du skal være fyrste over Israel.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, sarki ya yi yarjejjeniya da su a gaban Ubangiji, suka kuwa naɗa Dawuda sarki bisa Isra’ila.
Og alle Israels eldste kom til kongen i Hebron, og kong David gjorde en pakt med dem i Hebron for Herrens åsyn; og de salvet David til konge over Israel.
4 Dawuda yana da shekara talatin ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara arba’in.
David var tretti år gammel da han blev konge, og han regjerte i firti år.
5 A Hebron ya yi mulki a bisa Yahuda shekara bakwai da wata shida, a Urushalima kuma ya yi mulki a bisa Isra’ila da Yahuda shekara talatin da uku.
I Hebron regjerte han over Juda i syv år og seks måneder, og i Jerusalem regjerte han i tre og tretti år over hele Israel og Juda.
6 Sarki da mutanensa suka tafi Urushalima don su kai wa Yebusiyawan da suke zaune a can hari, Yebusiyawa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba; ko makafi da guragu kaɗai ma za su kore ka.” Suka yi tsammani suna cewa, “Dawuda ba zai iya shiga can ba.”
Så drog kongen og hans menn til Jerusalem mot jebusittene, som bodde der i landet; men de sa til David: Du kommer aldri inn her; blinde og lamme skal drive dig bort med de ord: David kommer aldri inn her.
7 Duk da haka, Dawuda ya kame kagarar Sihiyona, wadda ta zama Birnin Dawuda.
Men David inntok allikevel Sions borg, det er Davids stad.
8 A ranar, Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kame Yebusiyawa, dole yă yi amfani da wuriyar ruwa don yă kai ga waɗannan ‘guragu da makafi’ waɗanda suke abokan gāban Dawuda.” Shi ya sa suka ce, “‘Makafi da guragu’ ba za su shiga fadan sarki ba.”
Den dag sa David: Hver den som slår jebusittene og trenger frem til vannledningen og slår de lamme og blinde som hater David han skal være høvding og fører. Derav kommer det ord: En blind og en lam skal ikke komme inn i huset.
9 Sai Dawuda ya zauna a kagarar, ya kuma kira ta Birnin Dawuda. Ya gina wuraren da suke kewaye da ita, tun daga madogaran gini zuwa ciki.
David tok sin bolig i borgen og kalte den Davids stad; og David bygget rundt omkring fra Milo og innover.
10 Ya yi ta ƙara ƙarfi, gama Ubangiji Allah Maɗaukaki yana tare da shi.
David blev større og større, og Herren, hærskarenes Gud, var med ham.
11 To, Hiram sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda tare da gumaguman itacen al’ul, da kafintoci, da kuma maginan duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda fada.
Og Hiram, kongen i Tyrus, skikket sendemenn til David med sedertre, og han sendte tømmermenn og stenhuggere; og de bygget et hus for David.
12 Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya naɗa shi sarki bisa Isra’ila, ya kuma ɗaukaka masarautarsa saboda mutanensa Isra’ila.
Og David forstod at Herren hadde stadfestet hans kongedømme over Israel, og at han hadde hevet hans rike høit for sitt folk Israels skyld.
13 Bayan ya bar Hebron, Dawuda ya ƙara ɗauko wa kansa waɗansu ƙwarƙwarai da mata a Urushalima. Aka haifa masa’ya’ya maza da mata.
David tok ennu flere medhustruer og hustruer fra Jerusalem efterat han var kommet fra Hebron, og han fikk ennu flere sønner og døtre.
14 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
Dette er navnene på de sønner han fikk i Jerusalem: Sammua og Sobab og Natan og Salomo
15 Ibhar, Elishuwa, Nefeg, Yafiya,
og Jibbar og Elisua og Nefeg og Jafia
16 Elishama, Eliyada da Elifelet.
og Elisama og Eljada og Elifelet.
17 Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
Da filistrene hørte at David var blitt salvet til konge over Israel, drog alle filistrene ut for å søke efter David; og da David hørte det, drog han ned til borgen.
18 To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
Og filistrene kom og spredte sig utover i Refa'im-dalen.
19 saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
Da spurte David Herren: Skal jeg dra ut mot filistrene? Vil du gi dem i min hånd? Og Herren svarte: Dra ut! Jeg vil gi filistrene i din hånd.
20 Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
Så kom David til Ba'al-Perasim, og der slo han dem, og han sa: Herren har brutt igjennem mine fiender foran mig, som vann bryter igjennem. Derfor blev dette sted kalt Ba'al-Perasim.
21 Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
Der lot de efter sig sine avgudsbilleder, og David og hans menn tok dem med sig.
22 Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;
Men filistrene drog ut ennu en gang og spredte sig utover i Refa'im-dalen.
23 saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.
Og David spurte Herren, men han sa: Du skal ikke dra dit op; gå omkring så du kommer bakenfor dem, og gå så på dem midt for baka-trærne,
24 Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”
og når du hører lyden av skritt i baka-trærnes topper, da skynd dig! For da har Herren draget ut foran dig for å slå filistrenes hær.
25 Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.
David gjorde således som Herren hadde befalt ham; og han slo filistrene og forfulgte dem fra Geba til bortimot Geser.

< 2 Sama’ila 5 >