< 2 Sama’ila 5 >

1 Dukan kabilar Isra’ila suka zo wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu nama da jininka ne.
Et toutes les tribus d’Israël vinrent vers David à Hébron, disant: Nous voici, nous sommes votre os et votre chair.
2 A dā da Shawulu yake sarauta a bisanmu, kai ne kake bi Isra’ilawa zuwa yaƙe-yaƙensu. Ubangiji kuwa ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayi mutanena Isra’ila, za ka kuma zama sarkinsu.’”
Mais et hier et avant-hier, lorsque Saül était roi sur nous, vous meniez et rameniez Israël; mais le Seigneur vous a dit: C’est toi qui seras le pasteur de mon peuple Israël, et c’est toi qui seras chef sur Israël.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, sarki ya yi yarjejjeniya da su a gaban Ubangiji, suka kuwa naɗa Dawuda sarki bisa Isra’ila.
Et les vieillards d’Israël vinrent aussi vers le roi à Hébron, et le roi David fit alliance avec eux à Hébron devant le Seigneur, et ils oignirent David roi sur Israël.
4 Dawuda yana da shekara talatin ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara arba’in.
David était âgé de trente ans, lorsqu’il commença à régner, et il régna quarante ans.
5 A Hebron ya yi mulki a bisa Yahuda shekara bakwai da wata shida, a Urushalima kuma ya yi mulki a bisa Isra’ila da Yahuda shekara talatin da uku.
À Hébron, il régna sur Juda sept ans et six mois; mais à Jérusalem, il régna trente-trois ans sur tout Israël et Juda.
6 Sarki da mutanensa suka tafi Urushalima don su kai wa Yebusiyawan da suke zaune a can hari, Yebusiyawa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba; ko makafi da guragu kaɗai ma za su kore ka.” Suka yi tsammani suna cewa, “Dawuda ba zai iya shiga can ba.”
Et le roi s’en alla, et tous ceux qui étaient avec lui, à Jérusalem, contre les Jébuséens, habitants du pays: et ceux-ci dirent à David: Vous n’entrerez pas ici, à moins que vous n’enleviez les aveugles et les boiteux, disant par là: David n’entrera pas ici.
7 Duk da haka, Dawuda ya kame kagarar Sihiyona, wadda ta zama Birnin Dawuda.
Mais David prit la citadelle de Sion, qui est la cité de David.
8 A ranar, Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kame Yebusiyawa, dole yă yi amfani da wuriyar ruwa don yă kai ga waɗannan ‘guragu da makafi’ waɗanda suke abokan gāban Dawuda.” Shi ya sa suka ce, “‘Makafi da guragu’ ba za su shiga fadan sarki ba.”
Car David avait proposé en ce jour-là une récompense à celui qui battrait les Jébuséens, toucherait les gouttières des toits, et enlèverait les aveugles et les boiteux, haïssant l’âme de David. C’est pourquoi l’on dit en proverbe: Un aveugle et un boiteux n’entreront point dans le temple.
9 Sai Dawuda ya zauna a kagarar, ya kuma kira ta Birnin Dawuda. Ya gina wuraren da suke kewaye da ita, tun daga madogaran gini zuwa ciki.
Or, David habita dans la citadelle, et il l’appela Cité de David; et il bâtit tout autour, depuis Mello et au dedans.
10 Ya yi ta ƙara ƙarfi, gama Ubangiji Allah Maɗaukaki yana tare da shi.
Et il allait, avançant et croissant; et le Seigneur Dieu des armées était avec lui.
11 To, Hiram sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda tare da gumaguman itacen al’ul, da kafintoci, da kuma maginan duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda fada.
Hiram, roi de Tyr, envoya aussi des messagers à David, des bois de cèdre, des charpentiers et des tailleurs de pierres pour les murailles; et ils bâtirent une maison à David.
12 Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya naɗa shi sarki bisa Isra’ila, ya kuma ɗaukaka masarautarsa saboda mutanensa Isra’ila.
Et David connut que le Seigneur l’avait confirmé roi sur Israël, et qu’il avait élevé son royaume sur son peuple Israël.
13 Bayan ya bar Hebron, Dawuda ya ƙara ɗauko wa kansa waɗansu ƙwarƙwarai da mata a Urushalima. Aka haifa masa’ya’ya maza da mata.
David prit donc encore des femmes du second et du premier rang de Jérusalem, après qu’il fut venu d’Hébron; et il naquit à David d’autres fils et des filles;
14 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
Et voici les noms de ceux qui lui naquirent à Jérusalem: Samua, Sobab, Nathan, Salomon,
15 Ibhar, Elishuwa, Nefeg, Yafiya,
Jébaar, Elisua, Népheg,
16 Elishama, Eliyada da Elifelet.
Japhia, Elisama, Elioda et Eliphaleth.
17 Da Filistiyawa suka ji labari an shafe Dawuda sarki a bisa Isra’ila, sai suka haura da ƙarfi sosai don su nema shi, amma Dawuda ya ji labarin sai ya gangara zuwa mafaka.
Les Philistins donc apprirent qu’on avait oint David comme roi sur Israël, et ils montèrent tous pour chercher David; lorsque David l’eut appris, il descendit dans la forteresse.
18 To, fa, Filistiyawa suka zo suka baje ko’ina a cikin Kwarin Refayim;
Or, les Philistins, venant, se répandirent dans la vallée de Raphaïm.
19 saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In tafi in kai wa Filistiya hari? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Je ka, gama tabbatacce zan bashe Filistiyawa a hannunka.”
Et David consulta le Seigneur, disant: Monterai-je contre les Philistins, et les mettrez-vous en ma main? Et le Seigneur dit à David: Monte, parce que les livrant, je mettrai les Philistins en ta main.
20 Saboda haka Dawuda ya tafi Ba’al-Ferazim, a can ya ci su da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa yakan fasu, haka Ubangiji ya kakkarya abokan gābana a gabana.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
David donc vint à Baal-Pharasim, et il les battit là, et il dit: Le Seigneur a dispersé mes ennemis devant moi, comme se dispersent les eaux. C’est pour cela que ce lieu fut appelé du nom de Baal-Pharasim.
21 Filistiyawa suka bar gumakansu a can, Dawuda da mutanensa kuwa suka kwashe su.
Et les Philistins laissèrent là leurs images taillées au ciseau, que David et ses hommes emportèrent.
22 Har yanzu Filistiyawa suka sāke haurawa suka bazu a Kwarin Refayim;
Et les Philistins recommencèrent encore à monter, et ils se répandirent dans la vallée de Raphaïm.
23 saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya kuwa ce, “Kada ka haura kai tsaye, amma ka kewaya ta bayansu ka fāɗa musu a gaban itatuwan balsam.
Alors David consulta le Seigneur: Monterai-je contre les Philistins, et les livrerez-vous en mes mains? Le Seigneur répondit: Ne monte pas contre eux, mais tourne derrière eux, et tu viendras contre eux vis-à-vis des poiriers.
24 Da zarar ka ji tafiya kamar na takawar sojoji tana a bisan itatuwan balsam, sai ka yi maza, gama wannan alama ce cewa Ubangiji ya sha gabanka don yă karkashe sojojin Filistiyawa.”
Et lorsque tu entendras le bruit de quelqu’un qui marche au haut des poiriers, tu engageras la bataille, parce qu’alors marchera le Seigneur devant ta face pour battre le camp des Philistins.
25 Saboda haka Dawuda ya aikata yadda Ubangiji ya umarce shi, ya kuma karkashe Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.
C’est pourquoi David fit comme lui avait ordonné le Seigneur, et il battit les Philistins depuis Gabaa jusqu’à ce qu’on arrive à Gézer.

< 2 Sama’ila 5 >