< 2 Sama’ila 4 >
1 Sa’ad da Ish-Boshet ya ji labari cewa Abner ya mutu a Hebron, sai ya karaya, sai dukan hankalin Isra’ila ya tashi.
Quando o filho de Saul soube que Abner estava morto em Hebron, suas mãos ficaram fracas, e todos os israelitas ficaram perturbados.
2 To, ɗan Shawulu yana da’ya’ya maza biyu da suke shugabannin’yan hari. Ana kiran ɗaya Ba’ana, ɗayan kuma Rekab. Su’ya’yan Rimmon mutumin Benyamin ne daga Beyerot, an lissafta Beyerot a ɓangaren Benyamin,
O filho de Saul tinha dois homens que eram capitães de bandas de assalto. O nome de um era Baaná e o nome do outro Rechab, os filhos de Rimmon, o Beerotita, dos filhos de Benjamim (pois Beerote também é considerado parte de Benjamim;
3 domin mutanen Beyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.
e os Beerotitas fugiram para Gittaim, e viveram como estrangeiros até hoje).
4 (Yonatan ɗan Shawulu yana da ɗa mai suna Mefiboshet wanda yake gurgu a duka ƙafafu. Yana da shekara biyar ne sa’ad da labarin mutuwar Shawulu da Yonatan ya zo daga Yezireyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi ta gudu, amma yayinda take hanzari tă gudu, sai ya fāɗo, ya gurgunce.)
Agora Jonathan, filho de Saul, tinha um filho que era coxo nos pés. Ele tinha cinco anos quando a notícia sobre Saul e Jonathan saiu de Jezreel; e sua enfermeira o pegou e fugiu. Quando ela se apressou a fugir, ele caiu e ficou coxo. Seu nome era Mephibosheth.
5 To, Rekab da Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, suka tafi gidan Ish-Boshet, suka isa can da tsakar rana yayinda yake hutun tsakar rana.
Os filhos de Rimmon, o Beerothite, Rechab e Baanah, saíram e chegaram por volta do calor do dia à casa de Ishbosheth enquanto ele descansava ao meio-dia.
6 Suka shiga sashe na cikin gida sai ka ce suna so su ɗibo alkama ne, suka soke shi a ciki. Sa’an nan Rekab da Ba’ana ɗan’uwansa suka zame suka ɓace.
Eles chegaram lá no meio da casa como se tivessem buscado trigo, e o atingiram no corpo; e Rechab e Baanah, seu irmão, escaparam.
7 Sun shiga gidan yayinda yake kwance a gado a ɗakin barcinsa. Bayan sun soke shi sai suka kashe shi, suka kuma datse kansa. Suka ɗauke shi, suka yi tafiya dukan dare suka bi ta Araba.
Agora quando entraram na casa enquanto ele estava deitado em sua cama em seu quarto, o atingiram, o mataram, o decapitaram e lhe tiraram a cabeça, e foram pelo caminho do Arabah a noite toda.
8 Suka kawo kan Ish-Boshet wa Dawuda a Hebron, suka ce wa sarki, “Ga kan Ish-Boshet ɗan Shawulu, maƙiyinka, wanda ya nemi yă kashe ka. A yau Ubangiji ya rama wa ranka yă daɗe sarki, a kan Shawulu da zuriyarsa.”
Eles trouxeram a cabeça de Ishbosheth para David em Hebron, e disseram ao rei: “Eis a cabeça de Ishbosheth, o filho de Saul, seu inimigo, que procurava sua vida! Javé vingou hoje meu senhor, o rei de Saul e de sua descendência”.”
9 Dawuda ya ce wa Rekab da ɗan’uwansa Ba’ana,’ya’yan Rimmon mutumin Beyerot, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya kuɓutar da ni daga wahala,
David respondeu a Rechab e Baanah, seu irmão, os filhos de Rimmon, o Beerotíco, e lhes disse: “Como Javé vive, que redimiu minha alma de toda adversidade,
10 sa’ad da wani mutum ya ce mini, ‘Shawulu ya mutu,’ yana tsammani ya kawo labari mai daɗi ne, na kama shi na kashe a Ziklag. Ladar da na ba shi ke nan saboda labarinsa!
quando alguém me disse: 'Eis que Saul está morto', pensando que trazia boas novas, eu o agarrei e o matei em Ziklag, que foi a recompensa que lhe dei por suas notícias.
11 Balle fa, sa’ad da mugayen mutane suka kashe marar laifi a gidansa, a bisa gadonsa, ashe, ba zan nemi jininsa daga hannunku in kawar da ku a duniya ba!”
Quanto mais, quando homens perversos mataram uma pessoa justa em sua própria casa, em sua cama, não deveria eu agora exigir seu sangue de sua mão, e livrar a terra de você”?
12 Saboda haka Dawuda ya umarci mutanensa, suka kuwa kashe su. Suka yayyanka hannuwansu da ƙafafunsu, suka kuma rataye jikunansu kusa da tafki a Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-Boshet suka binne a kabarin Abner a Hebron.
David comandou seus jovens, e eles os mataram, cortaram suas mãos e seus pés, e os penduraram ao lado da piscina em Hebron. Mas eles pegaram a cabeça de Ishbosheth e a enterraram no túmulo de Abner em Hebron.